Site icon Muryar 'Yanci – Labaru, Siyasa, Tsaro, Lafiya, Ilimi…

Za Mu Shafe Tarihin ‘Yan Ta’adda A Watan Disamba – Fadar Shugaban Kasa

Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa nan da watan Disamba za a kakkaɓe duk wata matsalar tsaron da ta dabaibaye Najeriya.

Aregbesola ya bada wannan tabbacin lokacin da ya ke tattaunawa da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), a Abuja.

Minista ya ce Shugaba Muhammadu Buhari ya bada wa’adin cewa lallai daga nan zuwa Disamba dukkan hukumomin tsaron su tabbatar da sun samar da dawwamammen zaman lafiya a dukkan faɗin ƙasar nan.

Ya ce Buhari ya ce ba zai sauka daga mulki ba tare da ya daƙile matsalar tsaron da ke neman durkusar da ƙasar nan ba.

“Shugaba Buhari ya bada wa’adin nan da watan Disamba cewa Hukumomin tsaro su kakkaɓe duk wata barazanar tsaron da ke addabar rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya nan zuwa watan Disamba.

“Na yi amanna cewa dukkan ɓangarorin tsaron ƙasar nan sun tashi tsaye haiƙan, babu sauran hutu, domin su tabbatar cewa sun kawar da duk wata barazanar tsaro a ƙasar nan.

Exit mobile version