Rahotanni daga Gusau babban birnin Jihar Zamfara na bayyana cewar Gwamnan Bello Mohammed Matawalle, ya sanar da cewa ranar Litinin ko Talata za’a mayar da layukan sadarwa da aka katse a jihar sakamakon matsalar tsaro.
Matawalle ya bayyana hakan ne yayin zaben Shugabannin jam’iyyar All Progressive Congress APC wanda ya gudana a Gusau babban birnin Jihar.
A taron, Gwamnan yace za’a dawo da sabis kuma mutane zasu koma cin kasuwanninsu na mako. Idan an tuna cewa a ranar 4 ga Satumba na wannan shekara an datse sabis domin shawo kan lamarin garkuwa da mutane da ya addabi jihar.
A cewarsa: “A bayanan da muka samu, an samu saukin hare-haren da ake kaiwa garuruwa kuma nan da Litinin ko Talata, kowa a jihar zai iya waya da jama’a.”