‘Yan Bindiga Sun Tafka Barna A Jihar Sokoto

Rahoton dake shigo mana daga jihar Sokoto na bayyana cewar wasu ‘yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai hari kauyen Raka da ke karamar hukumar Tangaza a jihar Sakkwato inda suka kona gidaje da kayan abinci da dama kafin su tafi da wasu dabbobin gida da ba a bayyana adadinsu ba.

An tattaro cewa ‘yan fashin sun kashe wata mata ‘yar shekara 120 da wasu ‘yan unguwar biyar.

Da aka tuntubi Hakimin yankin, Alhaji Sa’idu Wakili ta wayar tarho, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce duk da cewa ba a yi garkuwa da kowa ba, ‘yan bindigar sun kona kashi biyu bisa uku na gidaje da kayayyakin abinci da kuma satar shanu.

Ya bukaci gwamnatin tarayya da na jihohi da su kara zage damtse wajen magance matsalolin tsaro a yankin.

Hakimin ya kuma yi kira ga masu hannu da shuni da su samar da gagarumin hanyoyin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar yankin.

Shugaban riko na karamar hukumar Tangaza, Alhaji Ibrahim Lawal Junju tare da mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin tituna Engr. Mai Damma Tangaza ya ziyarci al’ummar garin tare da jajanta wa mutanen garin sannan ya kuma yi alkawarin mika sakamakon bincikensa ga gwamnati domin taimakon wadanda abin ya shafa.

Labarai Makamanta