Tsohon Sakataren Buhari Wada Maida Ya Rasu

Allah ya yi wa kwararren dan Jaridar nan, Alhaji Wada Maida rasuwa a daren jiya Litinin, bayan yar gajeruwar rashin lafiya. Wanda kafin rasuwar sa shi ne Mawallafin Jaridar nan ta Turanci da ake bugawa A Abuja (People’s Daily) Kuma shi ne Shugaban Kwamiti Kula Da Kamfanin Dillancin Labarai Nijeriya wato (NAN) har ila yau, yana cikin masu hannun jari a Jaridar (Daily Trust)

Zaa yi sallah zanaidarsa a yau Talata da misalin karfe daya na rana,a masallacin Area 1, za’a rufe shi a makabartar Gudu da ke Abuja.

Alhaji Wada Maida, dan asalin Jihar Katsina, yana da Shekaru sabain da haihuwa. Ya bar Mata da ‘yaya da jikoki.

Allah Ya Jikansa da Rahama

Labarai Makamanta