Makaman Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Na Hannuna – Hamza Al-Mustafa

Ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar adawa ta Action Alliance AA, Manjo Hamza Al-Mustapha mai ritaya ya ce hukumomin da aka kirkira a Najeriya domin yakar cin hanci da rashawa ba za su iya yakar rashawan ba kwata-kwata.

Da yake zantawa da gidan talabijin na Channels a ranar Talata, tsohon hadimin na marigayi Abacha ya ce idan aka zabe shi shugaban kasa a shekarar 2023 shi zai inganta hukumomin dake yaki da rashawa a Najeriya.

“A Najeriya, na yi imanin cewa, hukumomin da aikinsu na farko shine kula da tsaro, cin hanci da rashawa a Najeriya ba su wadata ba. Suna da kaskanci sosai; basu da tsari mai kyau.”

Ya kuma bayyana cewa, daga abubuwan da yake gani kan yadda yaki da rashawa yake a Najeriya, kamar dai zomo ne ke bin zaki a guje a daji. Ya kuma koka da cewa, abin bakin ciki ne a ce hukumomin yaki da cin hanci da rashawa ba sa hada kai da sauran hukumomin kasashen waje don tsarawa da gano kudaden da aka ketarar daga Najeriya.

Al-Mustapha ya kuma ce, yana da kwarin gwiwa da kwarjinin iya tunkara tare da hukunta kowane dan rashawa ko ma wanene a kasar nan, ba tare da tsoro ko wata fargaba ba.

“Idan kuna maganan kwarjini ne, nagodewa Allah, ba wai ina alfahari bane.” Hamza Al-Mustapha ya ce bai taba satar kudi ba ko daukan arzikin kasa, sai dai ya kare dukiyar kasar duk da matsin lamba da wasu suka yi masa.

Labarai Makamanta