Gwamnatin Tarayya a ranar Talata ta ce akwai yiwuwar yawan talakawa ya karu zuwa miliyan 109 nan da karshen shekarar 2022.
Ministar Kudi, Kasafi da Tsare-tsare, Zainab Ahmed, wacce ta bayyana hakan ta ce sabbin mutum miliyan 11 na iya fada wa kangin talauci a cikin shekarar sakamakon annobar COVID-19.
Ta yi wadannan kalaman ne a Abuja, a ci gaba da taron da ake yi kan annobar COVID-19 mai taken ‘Fadan karshe wajen yaki, tare da murmurewa daga annobar COVID-19’.
Ministar, wacce ta sami wakilcin Darakta Janar na Ofishin Kasafin Kudi, Ben Akabueze, ta ce akalla mutum miliyan biyu ne suka fada talauci a 2020 saboda yadda yawan jama’a ya zarce karfin tattalin arzikin kasa.
Ta kuma ce annobar ta COVID-19 da kuma karyewar tattalin arziki sun kara yawan wasu matalautan da kimanin miliyan 6.6, lamarin da ya kawo adadin zuwa miliyan 8.6 a cikin shekarar kawai.
“Hakan na nuni da yiwuwar karuwar talakawa a Najeriya daga miliyan 90 a 2020 zuwa miliyan 109 a 2022,” inji Zainab.
Ta alakanta kalubalen da yawan karuwar ayyukan da ba su da tabbas, wadanda ta ce su ma sun dada jefa jama’a cikin kangin talaucin.
You must log in to post a comment.