Hukumomin Saudiya sun bayyana ranar Alhamis 30 ga watan Yuli a matsayin ranar hawa Arafa, sakamakon rashin ganin jinjirin watan Zul Hajji a yau Litinin, abin da ke nuna cewar gobe watan Zul Kida zai cika 30.
Kotun Kolin Saudiya ta ce ranar Laraba mai zuwa za ta zama ranar 1 ga watan Zul Hijja saboda cikar watan Zul Kida, abin da ya sa za a hau Arafat ranar Alhamis 30 ga watan Yuli.
A karkashin wannan tsari, ranar Juma’a 31 ga watan Yuli ta kasance ranar babbar Sallah ko kuma Eid-el Adha.
Kimanin mutane dubu 1 ake sa ran za su gudanar da aikin hajjin bana saboda annobar coronavirus wadda ta tilasta wa mahukuntan Saudiya daukar matakin rage yawan mahajjata daga sassan duniya.
You must log in to post a comment.