Hukumar NCDC da ke ɗakile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutum 89 da suka kamu da korona a ranar Asabar.
Bauchi ne inda cutar ta fi kama mutane a ranar Asabar inda alƙalumman suka bayyana ƙarin mutum 26 da suka kamu da cutar.
Cutar ta kuma kama ƙarin mutum 17 a Edo da Abuja
Mutum 15 suka kamu a Legas inda cutar ta fi bazuwa a Najeriya.
An kuma samu ƙarin mutum 10 da cutar ta kama a jihar Filato, yayin da cutar ta kama mutum hudu a Kaduna.
You must log in to post a comment.