CORONA: Mutane 499 Sun Sake Harbuwa – NCDC

Hukumar Yaki da Yaduwar Cututtuka a Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 499 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11.40 na daren ranar Alhamis 9 ga Yulin shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 499 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-157

Edo-59

Ondo-56

Oyo-31

Akwa Ibom-22

Borno-21

Plateau-19

Kaduna-18

Katsina-18

Bayelsa-17

FCT-17

Delta-14

Kano-11

Rivers-10

Enugu-8

Ogun-6

Kwara-4

Imo-3

Nasarawa-2

Osun-2

Abia-1

Ekiti-1

Niger-1

Yobe-1

30748 ne jimmilan wadanda suka kamu

12546 aka sallama kawo yanzu

689 sun mutu

Labarai Makamanta