CORONA: Mutane 160 Sun Sake Harbuwa – NCDC

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 160 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:27 na daren ranar Jumaa 28 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 160 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Plateau-44

Lagos-27

Katsina-18

Edo-15

Abuja-14

Ondo-10

Oyo-9

Kwara-6

Abia-4

Nasarawa-4

Kano-3

Ekiti-2

Kaduna-2

Kebbi-1

Jimillar wadanda suka kamu – 53,477

Jimillar wadanda suka warke – 41,017

Jimillar wadanda cutar ta kashe – 1,011

Labarai Makamanta