CORONA: Mutane 125 Sun Sake Harbuwa A Najeriya – NCDC

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 125 a fadin Najeriya.

Kwana takwas a jere yanzu jihar Plateau na zarce Legas da Abuja wajen yawan adadin sabbin wadanda suka kamu da cutar.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Alhamis 3 ga Satumba, shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 125 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Lagos-42

Abuja-25

Katsina-14

Kaduna-11

Kwara-8

Ondo-7

Delta-4

Anambra-3

Oyo-3

Edo-2

Ogun-2

Osun-2

Cross River-1

Labarai Makamanta

Leave a Reply