Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi hasashen manyan matsalolin da sabon shugaban Najeriya zai fuskanta inda ya kama aiki, El-Rufai ya ce dole ne wanda zai karbi mulkin kasar nan ya yi kokarin shawo kan matsalar tattalin arziki. Gwamna Nasir El-Rufai ya ce don haka akwai bukatar a magance matsalar tallafin man fetur da kuma tashin da kudin kasar waje suke yi a halin yanzu. Gwamnan na Kaduna ya ce idan shugaban kasar da aka zaba ya yi…
Cigaba Da KarantawaCategory: Tattalin Arziki
Tattalin Arziki
Mun Karbo Naira Biliyan 30 A Hannun Dakataccen Akanta Janar
Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban Hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon-kasa, ya ce zuwa yanzu an karbe N30bn daga hannun Idris Ahmed tsohon Akanta Janar na Æ™asa. Wadannan biliyoyi su na cikin N109bn da ake zargin Idris Ahmed ya karkatar a lokacin yana rike da ofishin Akanta Janar na kasa. Shugaban hukumar ta EFCC, Abdulrasheed Bawa ya shaidawa Duniya wannan a lokacin da ya halarci wani taro da aka yi da manema labarai a birnin tarayya Abuja.…
Cigaba Da KarantawaTakaita Cire Kudi Zai Rage Wa ‘Yan Siyasa Sharholiya – Sanusi
Khalifa Muhammad Sanusi , ya ce matakin da babban bankin Najeriya ya dauka na takaita cirar kudaden zai fi yin tasiri a kan `yan siyasa kasar fiye da talakawa. Ya bayyana hakan ne a karshen karatun Madaris da ya saba yi duk karshen mako. Ya ce `yan siyasar kasar na amfani da kudi a lokacin zabe don sayen kuri’un jama’a, lamarin da ke haifar da koma-baya ga kasar. Muhammadu Sanusi na II ya ce “abin takaici ne yadda mutane za su yi shekara hudu suna kwasar dukiyar al’umma, suna barin…
Cigaba Da KarantawaMun Tura Sabbin Takardun Naira Bankuna – Gwamnan Babban Banki
Gwamnan Babban Bankin Ƙasa, CBN, Godwin Emefiele, ya ce sabbin takardun kudi na Naira da aka canja wa fasali tuni sun isa bankuna kuma su na jiran a bada umarnin fara fitar da su. A cewar wata sanarwa da CBN ya wallafa a shafinsa na Twitter, Emefiele ya bayyana haka ne a Daura yayin da ya kai ziyarar yi wa shugaban kasa Muhanmadu Buhari karin bayani kan sake fasalin kudin Naira da kuma manufar hada-hadar kuÉ—i ta hanyar sadarwa da aka sake dawo da ita. Ya ce sake fasalin kudin…
Cigaba Da KarantawaMatsalar Mai: DSS Ta Ba NNPC Wa’adin Awa 48
Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta bai wa kamfanin man NNPC da kungiyar dalilan man fetur ta IPMAN wa’adin sa’o’i 48 su tabbatar da wadatuwar fetur a fadin kasar. Kakakin DSS, Peter Afunanya, ne ya fitar da sanarwar a Abuja bayan ganawar sirri da masu ruwa da tsaki a harkokin fetur. Sanarwar ta ce NNPC ta tabbatar da cewa tana da wadataccen fetur jibge da zai wadatar da ‘yan kasar har bayan bukukuwa karshen shekara. Ya ce an baza jami’an DSS a kowanne kusurwa na kasar domin hukunta duk…
Cigaba Da KarantawaKayyade Cire Kudi: Majalisa Ta Bukaci Babban Banki Da Yin Taka Tsan-Tsan
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar wasu Æ´an majalisar dattawa sun nuna fargaba game da matakin babban bankin Æ™asar na taÆ™aita kuÉ—in da al’umma za su iya cirewa daga asusun ajiya. Shugaban marasa rinjaye na majalisar Phillip Aduda ya janyo hankalin wakilan majalisar kan cewa matakin na CBN zai yi illa ga al’umma musamman ma masu Æ™ananan sana’o’i. A nasa tsokacin, shugaban majalisar Sanata Ahmed Lawan ya ja hankalin bankin na CBN da ya yi nazari kan lamarin kafin yanke hukunci kai-tsaye, kasancewar matakin zai…
Cigaba Da KarantawaBabban Bankin Kasa Ya Takaita Adadin Kudin Da ‘Yan Najeriya Za Su Cire A Bankuna
Babban bankin Najeriya CBN ya fitar da sababbin dokoki na hada-hadar kuÉ—aÉ—e a bankunan Æ™asar. A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, CBN ya taÆ™aita yawan kuÉ—ade laÆ™adan da Æ´an Æ™asar za su iya cirewa daga asusun ajiyarsu na banki. Wannan sanarwa na zuwa ne mako biyu bayan da Shugaba Muhammadu Buhari ya Æ™addamar da sabbin takardun naira da aka sabunta. Sabbin matakan da CBN É—in ya fitar a ranar Talata sun haÉ—a da: Yawan kuÉ—in da mutum É—aya zai iya fitarwa a banki a sati shi ne naira…
Cigaba Da KarantawaAl-Mundahana: Buhari Ya Kori Shugaban Hukumar NIRSAL
An tsige Manajan Darakta na Hukumar rarraba tallafi a fannin Aikin Gona na kasa (NIRSAL) daga aikinsa. Kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito Majiyar Dimokuradiyya ta nakalto cewa korar Aliyu Abdulhameed, ba zai rasa nasaba da zarge-zargen cin hanci da rashawa da yawa ba. A watan Janairun bana ne Daily Trust ta gudanar da bincike kan yadda NIRSAL ke bayar da lamunin rancen biliyoyin Naira na wasu kamfanoni masu zuba jari don noma hekta 20,000 na alkama na noman rani a Kano da kuma Jigawa bisa zargin karkatar da…
Cigaba Da KarantawaEFCC Ta Sake Bankado Zunubban Tsohuwar Ministar Mai
Hukumar EFCC ta ce binciken da ta gudanar ya nuna cewa, Diezani Madueke, tsohuwar ministar albarkatun man fetur, ta bai wa ‘yan siyasa dala miliyan 115 domin yin magudin zaben shekarar 2015. Shugaban Hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa ne ya bayyana haka a ranar Laraba nan a wani taron karrama sabbin kwamishinonin zabe (INEC) da aka yi a Legas. Bawa wanda ya samu wakilcin Adukwu Michael baban darakta a hukumar mai kula da sashen binciken laifuka, ya bayyana wannan rashin gaskiya da tsohowar ministar ta aikata a matsayin babban abin takaici…
Cigaba Da KarantawaCushe A Kasafin Kudi: An Raba Rana Tsakanin Ministar Jin Kai Da Ministar Kudi
Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar batun yi wa kasafin kudin 2023 ciko da majalisar dattawan ke tuhumar ma’aikatar kudi na ci gaba tayar da kura. Kan wannan batun, Ministar jin kai ta aika wa takwararta ta ma’aikatar kudi wata wasika wadda a ciki ta dora alhakin bayyanar wasu naira biliyan 206 cikin kasafin kudin ma’aikatarta, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce tsakanin wadannan ma’aikatun gwamnatin biyu. A makon jiya, yayin da ministar jin kai ta halarci zaman majalisar dattawa domin kare kasafin kudin ma’aikatarta,…
Cigaba Da KarantawaMun Yi Nasara A Shari’o’i Fiye Da 3000 A Bana – EFCC
Hukumar EFCC mai yaÆ™i da cin hanci da rashawa a ta ce ta yi nasara a shari’o’i 3,328 da ta gurfanar da mutanen da take zargi da cin hanci cikin wata 11 na shekarar 2022. Shugaban hukumar Abdulrasheed Bawa ya bayyana cewa ya zuwa 18 ga watan Nuwamba 2022, sun yi nasarar Æ™wace kuÉ—i naira miliyan 755 daga hannun tsohon babban akanta na Æ™asa waÉ—anda suka mayar wa gwamnati. Kazalika, EFCC ta Æ™wace kadarorin alfarma uku daga hannun Kanar Bello Fadile (mai ritaya) – tsohon mataimaki na musamman ga tsohon…
Cigaba Da KarantawaEFCC Ta Sake Gurfanar Da Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Gaban Kuliya
Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC ta sake gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Mukhtar Ramalan Yero a gaban babbar kotun tarayya da ke Kaduna kan wasu zarge-zargen da ke da alaka da halasta kudin haram. Hukumar na zargin tsohon gwamnan tare da wasu mutum uku da karbar cin hancin kudi da suka kai naira miliyan 700 daga hannun tsohuwar ministar albarkatun man fetur Diezani Alison-Madueke domin yin magudin zaben shugaban kasa na shekarar 2015. Sauran mutum ukun da ake tuhumarsu tare da tsohon…
Cigaba Da KarantawaBankin Bada Lamuni Ya Nemi A Gudanar Da Bincike Kan NNPC
Bankin Bada Lamuni na Duniya IMF ya bukaci gwamnatin tarayya da ta kaddamar da bincike akan man fetur din da kamfanin NNPC ya ce ana sha a cikin kasar da kuma irin kudaden tallafin da ake zubawa da sunan talaka. IMF ya kuma bukaci bincike akan kudaden da kamfanin ke zubawa a lalitar gwamnati sakamkon irin gibin da ya gani bayan ziyarar aikin da jami’ansa suka kammala a Najeriya. Hukumar ta ce abin takaici ne yadda kamfanin ke tafka asara sakamakon kashe makudan kudade da biyan dimbin basussuka, yayin da…
Cigaba Da KarantawaKotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Badakalar Cire Ciyawa
Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta wanke tsohon sakataren gwamnatin tarayya Mista Babachir Lawal da wasu mutum biyar daga zargin wata badaÆ™ala ta kuÉ—i naira miliyan 544. Hukumar yaÆ™i da cin hanci da yi wa tattalin arziÆ™in Æ™asa zagon Æ™asa ta Najeriya, EFCC ce ta gurfanar da mutanen, tana zargin su da almundahana kan wata kwangilar cire ciyawa, wadda kuÉ—inta ya kai naira miliyan 544. Mai sharia’a Charles Agbaza ya ce babu wani abu da zai nuna cewa Babachir yana da laifi a cikin bayanan da shaidu 11…
Cigaba Da KarantawaSauya Takardun Naira: Mun Gano Gwamnoni Masu Kuruciyar Bera – EFCC
Shugaban hukumar hana cin hanci da rashawa a Najeriya, Abdulrasheed Bawa ya bayyana cewa, adadin gwamnonin da hukumarsa ke sa ido a kansu bisa zargin tara kudin haram ya karu. Bawa ya bayyana hakan ne a fadar shugaban kasa bayan ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari, dangane da irin nasarorin da hukumar tashi ta samu. Bawa ya ki bayyana adadin gwamnonin ko sunayensu, inda yace ba ya son a yi masa mummunar fahimta ko a sauya mishi magana. An ce gwamnonin suna kokarin fara fitar da kudaden tare da tabbatar…
Cigaba Da KarantawaSauya Takardun Naira: Za A Sanya Idanu Kan Masu Kai Kudi Banki
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Ministar tattalin arziki, kasafi da tsare-tsaren kudi ta Najeriya, Zainab Shamsuna Ahmed tayi karin haske game da sababbin kudi da za a buga. A wani bayani da aka fitar a shafin LinkedIn a ranar Alhamis, an fahimci ba haka nan za a kyale mutane su rika maida kudin hannunsu cikin bankuna ba, ba tare da sa ido ba musanman daga Hukumar EFCC. Ministar tace za a hukunta duk bankin da ya sabawa ka’idojojin da aka gindaya, Ministar ta bayyana…
Cigaba Da KarantawaTashin Dala: EFCC Ta Damke ‘Yan Canji A Biranen Abuja Da Legas
Hukumar Yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC, ta kama ‘yan canji 87 a babban birnin kasar Abuja da kuma jihohin Lagos da Kano a ci gaba da kokarin kawo karshen matsalar karanci da tashin farashin Dala da ake fuskanta a kasar. An ruwaito cewar jami’an hukumar EFCC sunyi dirar mikiya a wasu daga cikin wuraren canjin kudi da ke Abuja tare da kama mutane 25 masu gudanar da harkar ta haramtatciyar hanya wanda ya ke zuwa bayan kama wasu 40, adadin da ya nuna cewa mutane 65 ke nan…
Cigaba Da KarantawaMun Samu Gagarumar Nasara A Shekarar Bana – EFCC
Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Hukumar EFCC mai yaki da rashin gaskiya tayi nasarar daure mutane 2, 847 da suka aikata laifuffukan damfara a shekarar bana. Shugaban EFCC na kasa, Abdulrasheed Bawa ya yi wannan bayani yayin da bayyana a gaban majalisar Æ™asa bada rahoton ayyukan hukumar. Abdulrasheed Bawa ya zauna da kwamitin yaki da rashin gaskiya na majalisar dattawa domin ya kare kasafin kudin hukumar na shekarar 2022/23. An yi wannan zama ne a bayan labule, sai bayan nan Bawa ya samu lokaci…
Cigaba Da KarantawaNuna Kwazo: Bankin Najeriya Ya Karrama Kamfanin Bizi Mobile
Babban Bankin kasa wato CBN, Karkashin jagorancin Shugaban bankin Mista Godwin Emefele, ya karrama kamfanin Bizi Mobile Cashless Consultant limited da lambar yabo a matsayin gwarzon kamfani mafi jajircewa da kwazo akan tallata shirin e-Naira a daukacin kasar baki daya. An shirya bikin karramawar da kuma kaddamar da sabon shirin Babban bankin kasa (CBN) mai taken ‘Digital currency (CBDC) e-Naira.’ wanda ya guda a dakin taro na Eko hotel dake Jihar lagos. A yayin da Shugaban Babban bankin kasa CBN, Mista Godwin Emefel, yake mika kambun lambar yabo ga Shugaban…
Cigaba Da KarantawaAdamawa: An Shawarci Gwamnatin Tarayya Da Ba Dillalan Mai Damar Shigo Mai
A wani mataki na magance karancin man fetur a fadin kasan nan baki daya. An sahawarci gwamnatin tarayyar Najeriya da ta sakarma dillalain man fetur masu zaman kansu mara domin samun damar shigo da mai din. Shugaban kwamitin amintattu na kungiyar dilalan man fetur mai zaman kanta a Najeriya IPMAN Alhaji Baba-Kano Jada ne yayi wanana kira a zantawarsa da Wakilinmu a Yola. Alhaji Baba-Kano Jada yace mafita daga cikin matsalalolin karanci dama tsadar man fetur a fadin Najeriya ita ce a ba kamfanoni masu zaman kansu lasisin izinin shigo…
Cigaba Da Karantawa