Ɗan takarar gwamnan Jihar Gombe a jam’iyyar NNPP, Khamisu Ahmed Mailantarki, ya na ci gaba da karɓar dandazon manya da ƙananan magoya bayan APC mai mulkin jihar da kuma PDP. A ƙarshen makon nan ne Mailantarki ya haska wa wasu manyan mambobin PDP hanya, su ka bi ta gwadaben da su ka koma NNPP. Mambobin dai zaratan magoya bayan fitaccen ɗan siyasar nan ne Jamil Isyaku Gwamna, waɗanda ake kiran ƙungiyar su da suna Sardauna Dawo-Dawo. A ranar Juma’a ce Mailantarki ya karɓi dandazon ‘yan PDP ɗin a bisa tarbar…
Cigaba Da KarantawaCategory: Siyasa
Siyasa
GOMBE 2023: Mailantarki Kwashe Baraden Yakin Isyaku Gwamna, Sun Koma NNPP
Daga Wakilin Mu Ɗan takarar gwamnan Jihar Gombe a jam’iyyar NNPP, Khamisu Ahmed Mailantarki, ya na ci gaba da karɓar dandazon manya da ƙananan magoya bayan APC mai mulkin jihar da kuma PDP. A ƙarshen makon nan ne Mailantarki ya haska wa wasu manyan mambobin PDP hanya, su ka bi ta gwadaben da su ka koma NNPP. Mambobin dai zaratan magoya bayan fitaccen ɗan siyasar nan ne Jamil Isyaku Gwamna, waɗanda ake kiran ƙungiyar su da suna Sardauna Dawo-Dawo. A ranar Juma’a ce Mailantarki ya karɓi dandazon ‘yan PDP ɗin…
Cigaba Da KarantawaYa Zama Dole A Daina Kai Wa Ofisoshinmu Hari – INEC
Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Farfesa Mahmoud Yakubu ya yi kira ga jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a kasar, da su yi duk abin da za su yi domin ganin an daina kai wa kayayyakin zaben 2023 hari a ko ina. Ya yi wannan kira ne lokacin da yake tattaunawa da majalisar wakilai da kuma kwamiin da yake bincike kan hare-haren da ake kaiwa kan kayayyakin hukumar. Ya ce hukumar ta fuskanci hare-hare 50 cikin jihohi 15 a 2019, Farfesa Yakubu ya bayyana wasu daga cikin…
Cigaba Da KarantawaZabena Ne Zai Share Wa Inyamurai Samun Zama Shugaban Kasa – Atiku
Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya ce shi tsani ne ga kabilar Igbo wajen fitar da shugaban kasar Najeriya daga cikinsu. Atiku, wanda ya yi magana a dandalin Alex Ekwueme, Akwa, a yayin taron gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a jihar Anambra, ya yi alkawarin taimakawa kabilar Igbo wajen fitar da shugaban kasa bayan wa’adinsa. “Zan zama matattakalar tabbatar da kabilar Igbo sun samu shugaban kasa muddin kuka zabe ni a 2023.” “Zaku iya tabbatar da hakan, in kun lura wannan…
Cigaba Da KarantawaKADUNA: Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Nasarar Takarar Uba Sani
Kotun daukaka kara dake zamanta a birnin tarayya Abuja ta yi watsi da karan da Sani Sha’aban ya shigar kan nasarar dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani a zaben fidda gwanin gwamnan jam’iyyar da aka gudanar a jihar. Kotun ta ce ta fahimci cewa, daukaka karar an yi ta ne ba bisa ka’ida ba, kuma bata cika abin da ake bukata na cancanta bisa dalilin haka ta yi watsi da ƙarar tare da tabbatar da nasarar Sanata Uba Sani. Sha’aban ya daukaka kara ne…
Cigaba Da KarantawaJirgin Yakin Zaben Atiku Zai Dira Jíhar Anambra Yau Alhamis
Rahoton dake shigo mana daga jihar Anambra na bayyana cewar Jam’iyyar PDP tace shiri ya yi nisa na karban ɗan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, a jihar ranar Alhamis domin gangamin yakin neman zaɓe. Daraktan kamfen Atiku/Okowa na jihar Anambra, Dakta Obiora Okonkwo ne ya bayyana haka a wurin taron manema labarai ranar Laraba a Awka. Yace wannan gangamin kaddamar da yakin neman zaben PDP da zai guda a Awka a yau zai tabbatar wa duniya cewa Anambra ta PDP ce gaba ɗaya babu maganar wata Jami’yya. Okonkwo yace jirgin…
Cigaba Da Karantawa2023: Gwamna Inuwa Ya Roki Gwambawa Da Yin Sak
Labarin dake shigo mana daga jihar Gombe na bayyana cewar Gwamnan jihar Alhaji Muhammad Inuwa Yahaya, ya roki jama’ar jihar su garzaya su karɓi Katin zabensu domin samun damar kaɗa wa APC kuri’unsu a 2023. Gwamnan yace ɗumbin ayyukan da ya zuba a mulkinsa na farko babban alama ce dake nuna dacewarsa musamman yadda ya maida hankali wajen yaye matsin da mutane ke ciki. Inuwa Yahaya ya yi wannan jawabin ne yayin kamfe a gundumomi 5 da suka haɗa ƙaramar hukumar Balanga ta arewa ranar Litinin. Da farko, gwamnan ya…
Cigaba Da KarantawaBa Zan Iya Zama Dan Majalisa Ba Saboda Ban Da Hakuri – El Rufa’i
Rahoton dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewar Gwamnan jihar Nasir El-Rufai ya nuna babu shi babu zuwa majalisar tarayya ta kasa bayan kammala wa’adin Mulki. An san Gwamnoni da yin takarar Sanata idan sun gama wa’adinsu a jihohi, sai dai anashi ɓangaren Malam Nasir El-Rufai yana cewa ya sha bam-bam da sauran gwamnoni yace bai da hakuri da jajircewar da ake bukata wajen aikin majalisa. Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a wajen wani taron ‘yan majalisa da cibiyar nazarin aikin majalisa da damukaradiyya watau NILDS ta…
Cigaba Da KarantawaTinubu Ya Ziyarci Birnin Gwari Kafin Fara Kamfe A Kaduna
Labarin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar ɗan takarar shugabancin ƙasa a karkashin jam’iyya mai mulki ta APC Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci Birnin-Gwari kafin fara yakin neman zabensa a Kaduna. Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da tawagarsa sun isa jihar Kaduna inda za su gudanar da yakin neman zabensa a jihar ta Kaduna a ranar Talata. Tinubun ya samu rakiyar abokin takararsa Sanata Kashim Shettima da babban daraktan yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Filato, Simon…
Cigaba Da KarantawaNa Bar PDP Har Abada – Obasanjo
Tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo, a ranar Asabar, ya bayyana cewa ba zai taba komawa jam’iyyar adawa ta PDP da siyasa ba gaba daya a rayuwarsa. Ya bayyana hakan ne yayin hira da shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu da sauran masu fada a ji a jam’iyyar da suka ziyarcesa ranar Asabar bayan ganawar sirrin da suka yi, a gidansa dake birnin Abeakuta na jihar Ogun. “Na fita harkar siyasa kuma babu abinda zai iya mayar da ni. Duk wanda ke son shawarata, zan bada saboda amfanin Najeriya.” “Duk abinda nayi…
Cigaba Da KarantawaZan Yi Mulki Na Adalci Idan Na Lashe Zabe – Tinubu
Labarin dake shigo mana daga birnin Ibadan na Jihar Oyo na bayyana cewar a ranar Lahadi, 11 ga watan Disamba, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu, ya ba yan Najeriya tabbacin cewa zai zamo mai gaskiya da adalci ga kowa. Tinubu ya bayar da tabbacin ne yayin da yake jawabi a wani taro da shugabannin Musulunci daga kudu maso yamma a Ibadan, babban birnin jihar Oyo a ƙarshen mako. Dan takarar na APC ya yaba ma shugabannin addini a kasar kan addu’o’i da suke ci gaba…
Cigaba Da KarantawaMatsalar Tsaro: INEC Za Ta Sauya Wa Rumfunan Zabe 357 Waje A Katsina
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta ce za ta mayar da rumfunan zabe 357, PUs, zuwa wuraren da babu tsaro saboda kalubalen tsaro a jihar Katsina. A cewar hukumar, ta dauki matakin ne domin bai waduk ‘yan gudun hijira, da ke jihar damar kaɗa kuri’unsu a zaben 2023. Kwamishinan zaɓe na jihar, Farfesa Ibrahim Yahaya Makarfi ne ya bayyana haka a yayin wani taron masu ruwa da tsaki a yau Juma’a a Katsina. Ya bayyana cewa, dokar zabe ta 2022 ta yi tanadin tsare-tsare a bayyane da…
Cigaba Da KarantawaNasarawa: Matasa Sun Yi Wa Shugaban APC Ature
Rahotannin dake shigo mana daga Lafiya babban birnin Jihar Nasarawa na bayyana cewar wasu fusatattun Matasa sun yi wa Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Sanata Abdullahi Adamu ihu a yayin wani gangamin taron Jam’iyyar da ya gudana a jihar. Shugaban IPAC mai kula da harkar jam’iyyu a jihar Nasarawa, Cletus Ogah Doma ya yi tir da abin da Matasan suka aikata inda yace ko kaɗan wannan ba abu ne da za a lamunce sake faruwar hakan anan gaba. Sai dai ya yi ƙarin haske akan labarin da ake yaɗawa na…
Cigaba Da KarantawaNa Tuba Da Yin Siyasa – Goodluck Jonathan
Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan ya ce ba zai sake tsaya wa takarar zabe domin neman kujerar shugaban kasa ba, domin yin haka zai dakushe kimarsa a idon jama’a. Jonathan wanda ke tsokaci akan wani littafin da aka wallafa akansa wanda ya mayar da hankali akan zamansa a fadar shugaban kasa, yace zubar da kimarsa ne ya koma yana rokon mutane domin marasa baya da kuma masa yakin neman zabe domin sake zama shugaban kasa. Tsohon shugaban yace muddin jama’a suka farka a baci suka ganshi ya sake zama shugaban…
Cigaba Da KarantawaZa Mu Bar Najeriya Idan Peter Obi Ya Fadi Zabe – Babachir Lawal
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, SGF, Babachir Lawal, ya ce shi da wasu jiga-jigan siyasa masu goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, za su koma Kamaru idan dan takarar ya fadi zaben shugaban kasa a 2023. Tsohon SGF ɗin ya bayyana haka ne a jiya Litinin yayin wata tattauna wa da Obi da masu ruwa da tsaki na LP daga Arewa maso Gabas a Abuja. Lawal, jigo a jam’iyyar APC mai mulki, ya kuma bayyana mamakinsa da cewa APC ba ta kore shi daga jam’iyyar ba,…
Cigaba Da KarantawaYobe: Nasarata Kan Ahmed Lawan Daga Allah Ne – Bashir Machina
Labarin dake shigo mana daga jihar Yobe na bayyana cewar Alhaji Bashir Machina, halastaccen ‘dan takarar kujerar Sanata a jam’iyyar APC a mazabar Yobe ta Arewa yace nasararsa a kotu akan Shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan daga Allah ne. A yayin gangamin zagayawa tare da mika godiya ga magoya bayansa, Lawan yace duk wanda zai kare hakkin jama’arsa dole ya ga kalubale Machina ya dauki alkawarin Tafiya da dukkan kananan hukumomi shida dake karkashin mazabarsa idan ya samu nasara a babban zaben dake tafe. Machina wanda ya bayyana hakan a…
Cigaba Da KarantawaMun Tara Kudin Da Dole Za Mu Ci Zabe A Katsina – Hadi Sirika
Ministan harkokin jiragen sama, Hadi Sirika yana ganin cewa babu wanda ya isa ya bige jam’iyyar APC mai mulki a babban zabe mai zuwa a jihar Katsina Mahaifar Shugaban ƙasa Buhari kuma Jihar da ya shi ya fito. A wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta a kwanan nan, an ji yadda Sanata Hadi Sirika yake cika baki da cewa APC ta tanadi kudin yakin zabe, kuma za ta yi amfani dasu wajen cin zaɓe. Hadi Sirika ya yi wannan jawabi ne a wajen bikin da aka shirya…
Cigaba Da KarantawaKu Taya Mu Tsare Ofisoshinmu: Rokon INEC Ga ‘Yan Najeriya
Shugaban Hukumar zaɓe mai zaman kanta Farfesa Mahmood Yakubu ya roƙi al’ummar Najeriya su taimaka wurin kare kadadrorin hukumar gabanin babban zaɓen ƙasar mai zuwa. Hakan na zuwa ne bayan hare-haren da aka kai wa wasu ofisoshin hukumar a baya-bayan nan. Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne a lokacin da ya gana da ƙungiyar dattijan yammacin Afirka, a ofishinsa da ke Abuja, a ranar Litinin. Shugaban na INEC ya ce babban abin da ake fargaba gabanin zaɓen mai zuwa shi ne matsalar tsaro. Ya ce “an kai hari a ofisoshinmu…
Cigaba Da KarantawaAmurka Ba Ta Hana Tinubu Shiga Kasar Ba – Kalu
Bulaliyar Majalisar Dattawa, Sanata Orji Kalu, ya ƙaryata raɗe-raɗin da wasu ke yi cewa Amirka ta hana ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Bola Tinubu bizar iznin shiga ƙasar ta. Kalu ya fito a shafin sa na Facebook, ya wallafa cewa, Tinubu ya ɗaga tafiyar ce don ƙashin kan sa, amma babu wanda ya hana shi shiga Amurka. “Tinubu zai bar Najeriya a ranar 4 Ga Disamba, inda zai dira Landan. A can zai gana da jama’a a katafaren ɗakin taron Chatham House,” inji Rundunar Kamfen ɗin TInubu. Ta ce…
Cigaba Da KarantawaZamfara: Matawalle Ya Bada Umarnin Hallaka Kusoshin Jam’iyyar Mu – PDP
Jam’iyyar PDP ta zargi gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da kafa wani gungun ƴan daba, tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro domin kawar da jiga-jigan jam’iyyar adawa a jihar, a daidai lokacin da ‘yan sanda su ka janye tsaron ɗan takarar gwamna na PDP a jihar, Dauda Lawal. Jam’iyyar ta kuma yi zargin cewa ‘yan sanda sun fara wani mumunan samame da nufin kamawa tare da tsare wasu manyan shugabannin jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, tare da yi musu ƙage. Da ya ke zantawa da manema labarai a ranar Juma’a,…
Cigaba Da Karantawa