2023: Tabbas Tinubu Ne Shugaban Kasa – Kingibe

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babagana Kingibe, ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Lagas, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ne shugaban kasar Najeriya na gaba a babban zaben da za a yi na shekarar 2023. Bola Tinubu dai shine ya yi nasarar lashe tikitin takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC mai mulki a zaben fidda gwaninta da ya gudana a Eagle Square a ranar Laraba, 8 ga watan Yunin shekarar da muke ciki. Jigon na APC kuma babban jagoran Jam’iyyar ya samu kuri’u 1,271 inda ya kayar da sauran abokan karawarsa su…

Cigaba Da Karantawa

Takara: Wankin Hula Zai Kai Ahmed Lawan Dare

Idan ba a manta ba Sanata Ahmed Lawan shugaban majalisar Dattawa ya fafata a zaɓen fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC rabar 8 ga watan Yuni. Kafin zaɓen an yi masa kyakyawar zaton cewa shina jam’iyyar ta ke so ta tsayar ɗan takarar ta amma kuma hakan bai yiwu ba. An ruwaito cewa wanda yayi nasara a zaɓen fidda gwani na kujerar Sanatan Bashir Machina ya ce ba zai sauka daga kujerar takara ba.

Cigaba Da Karantawa

Adamawa: An Bukaci Jama’a Su Guji Siyasar Kabilanci – Shugaban ‘Yan Kasuwar Arewa

A yayin da ake gudanar da bikin ranar dimukuradiyya a Najeriya an kira yi ‘yan Najeriya da a daina siyasar kabilanci, É“angaranci dama addini domin cigaban dimokuraÉ—iyya harma da cigaban Najeriya baki daya. Shugaban Kungiyar ‘yan kasuwar Arewacin Najeriya Alhaji Muhammed Ibrahim 86 ne yayi wannan kira a lokacin zantawarsa da wakilinmu a Yola Fadar gwamnatin jihar Adamawa. Alhaji Ibrahim yace ya kamata ‘yan Najeriya suyi karatun ta nutsu wajen daina siyasar kabilanci ko bangaranci dama addini wanda acewarsa yin siyasar kabilanci ba zai haifawa dimokuraÉ—iyya É—a mai ido ba.…

Cigaba Da Karantawa

Nasarawa: Rashin Cika Alkawari Ya Sa Deligates Fito Na Fito Da Dan Takarar Sanata

Daga Ishaq Saeed Hamza Kimanin makwannin biyu ke nan da kammala zaben fidda gwani na É—an kujerar sanata mai wakiltar Nasarawa ta yamma kujerar da shugaban jamiyyar APC na kasa Sanata Abdullahi Adamu ya bari bayan zama shugaban jamiyyar APC na kasa. ‘Yan siyasa uku ne suka yi hankoron samun nasarar gadar Abdullahi Adamu da suka hada daHonorabul Aliyu Wadada (Sarkin YaÆ™in Keffi)Honorabul Arch Shehu Tukur (Sarkin Fadan Keffi)Hon Barr. Labaran Magaji (Matawallen Toto). Kafin akai ga zaben fidda gwanin Honorabul Aliyu Wadada ya sanar da janye takararsa ‘yan awanni…

Cigaba Da Karantawa

INEC Ta Yi Watsi Da Dan Takarar Sanatan APC A Akwa-Ibom

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, ta yi watsi da zaben fidda gwanin da ya samar da Godswill Akpabio a matsayin ‘dan takarar kujerar sanata Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma karkashin jam’iyyar APC. Akpabio, wanda ya janye daga takarar shugabancin kasa yace a zabi Tinubu a zaben fidda gwanin APC, an bayyana shi matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na kujerar sanatan Akwa Ibom a ranar Alhamis. Kamar yadda sakamakon sake zaben ya nuna, Akpabio ya yi nasara inda ya samu kuri’u 478, yayin da DIG…

Cigaba Da Karantawa

Jahadin Dake Kan ‘Yan Najeriya Shi Ne Kawar Da APC – Atiku

Dan takarar shugaban kasa na Babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga yan Najeriya da su fatattaki jam’iyyar All APC daga mulki a babban zaben 2023 mai zuwa domin dawo da Najeriya cikin hayyacinta. Atiku ya yi wannan kira ne a ranar Lahadi, 12 ga watan Yuni, a cikin sakonsa na ranar dimokradiyya, yana mai cewa hakan shine babban jahadi kuma abin da za a iya sakawa jaruman dimokradiyyan kasar nan da shi. Dan siyasar ya yi imanin cewa wannan bukin lokaci ne da dukkan masu…

Cigaba Da Karantawa

Ranar Dimukuradiyya: Ku Mallaki Katin Zabe Domin Zabar ‘Yan Takara Na Kwarai – Ramalan

Shugaban Kamfanin ATAR Communication mamallakan gidajen Talabijin da Rediyo na Liberty Alhaji Ahmed Tijjani Ramalan, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su tabbatar sun mallaki katin zaÉ“e domin samun nasarar zaÉ“ar ‘yan takarar da suka dace a zaÉ“en dake tafe na 2023. Ramalan ya yi wannan kiran ne a sakon murnar ranar dimukuradiyya ta bana 12 ga Watan Yunin Shekarar 2023. Shugabàn Kamfanin na ATAR ya bayyana ranar DimukuraÉ—iyya a matsayin wata rana mai muhimmanci a Najeriya sannan ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga ‘yan Nijeriya…

Cigaba Da Karantawa

2023: Babu Matsala Idan Tinubu Ya Dauki Mataimaki Musulmi – Kayode

Tsohon Ministan Sufurin sama, Femi Fani-Kayode yace zai goyi bayan dan takaran shugaban kasan jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, koda ya zabi mataimaki Musulmi. Kayode ya bayyana hakan ne yayin hira a shirin ‘Politics Today’ na tashar ChannelsTV ranar Alhamis. Yace sam ba zai yiwu ace za’a cire addini daga cikin siyasa ba: “Matsala ne kuma wajibi ne mu yi wa mutane bayani idan muka yanke shawarar yin haka. Ba ni da matsala idan aka yi haka (Musulmi da Musulmi). idan dan takarar mu Tinubu ya zabi hakan zamu goya…

Cigaba Da Karantawa

INEC Ta Tura Karin Na’urorin Rijistar Zabe A Jihohi

Hukumar zaÉ“e mai zaman kanta ta Æ™asa INEC, ta ce ta yanke shawarar tura Æ™arin na’urorin yin rajistar zaÉ“e a wasu jihohi saboda cunkoso da ake samu a wuraren da ake Æ™orafe-Æ™orafe. Wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Juma’a ta ce ta lura cewa an fi samun cunkoson a jihohin Kano da Legas da kuma yankin Kudu maso Gabas, inda ta tura Æ™arin na’urorin 209. “Hukumar za ta ci gaba da sa ido kan aikin na tsawon kwanaki sannan ta sake duba ci gaban da aka samu,” a…

Cigaba Da Karantawa

‘Yan Adawa Suka Hanani Aiki Sosai – Gwamnan Kogi

Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello ya ce kararrrakin da ‘yan adawa suka kai shi kotu lokacin da ya lashe zaben gwamna a karon farko su ne suka hana shi aiki sosai a jihar. Ya bayyana haka ne a cikin shirin A Fada A Cika, na gidan Rediyon BBC Hausa. Gwamna Yahaya Bello ya Æ™ara da cewar “Nasarar da muka samu a karo na biyu ta fi ta shekara hudu da muka yi a baya… mun yi aiki sosai amma saboda an kai mu kotu, an raba mana hankali. “Shari’u ashirin…

Cigaba Da Karantawa

Fidda Gwani: Osinbajo Ya Shiga Rudani Bayan Shan Kaye

Mataimakin Shugaban Æ™asa Osinbajo ya yi warwas a zaÉ“en fidda gwani na jam’iyyar APC inda tsohon ubangidansa kuma jigon jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya samu kuri’u 1,271 kuma ya tabbata ‘dan takara shugabancin kasa a zaben 2023 mai zuwa a APC. Kafin zaben, masu nazarin al’amurra sun yi ittifakin cewa ta yiwu Osinbajo ya sha wuya tunda a bayyane ya kalubalanci tsohon ubangidansa, jigon siyasar kasar Yarbawa kuma ‘dan takarar da yayi nasarar samun tikitin APC. Kin goyon bayansa a bayyane da Buhari ya yi A yayin da ya…

Cigaba Da Karantawa

Nasarar Tinubu Alama Ce Ta Samun Karbuwa A Arewa – Ganduje

Mai girma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano, ya taya Asiwaju Bola Tinubu, tsohon gwamnan Legas, murnar samun nasarar lashe zaben fidda gwani na shugaban kasa a jam’iyya mai mulki ta APC. A cikin wata sanarwa da Abba Anwar, babban sakataren watsa labarai na gwamnan ya fitar, na bayyana Ganduje ya ce nasarar da Tinubu ya samu a zaben fidda gwanin alama ce da ke nuna ya samu karbuwa a arewa da Æ™asa baki daya. Gwamnan na Kano kuma ya ce nasarar ta Tinubu za ta karfafa jam’iyyar kuma…

Cigaba Da Karantawa

NNPP Ta Tsayar Da Kwankwaso Takarar Shugabancin Kasa

Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka yi a ranar Laraba. Kwankwaso ya yi nasarar zama dan takarar shugaban kasar na NNPP ne bayan daligets 774 daga jihohi 36 sun sahale masa gaba daya ba tare da hamayya ba. Idan za a iya tunawa, shugaban jam’iyyar na NNPP na kasa, Boniface Aniegbonam, ya ce Kwankwaso shine dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar…

Cigaba Da Karantawa

2023: Ka Da Kuyi Gangancin Sake Zabar PDP – Wasiyyar Buhari Ga ‘Yan Najeriya

Mai girma Shugaban Æ™asa Muhammadu Buhari ya yi kira ga ‘yan Najeriya su tabbata ba su bar jam’iyyar adawa ta PDP “ta mayar da Æ™asa baya ba”. Da yake jawabi a wurin zaÉ“en É—an takarar shugaban Æ™asa na jam’iyyarsu ta APC, Buhari ya ce APC ta sauya Najeriya ta hanyar gudanar da ayyukan raya Æ™asa. “Wajibi ne mu zaÉ“i masu adalci ‘yan kishin Æ™asa da ke da aÆ™idar haÉ—a kan Æ™asarmu…don ciyar da ita gaba. “Bai kamata mu Æ™yale PDP ta mayar da Najeriya baya ba.” Zuwa lokacin haÉ—a wannan…

Cigaba Da Karantawa

Babban Abin Da Zan Aiwatar Da Zarar Na Yi Nasara – Tinubu

Labarin dake shigo mana daga filin Eagles Square dake birnin tarayya Abuja inda ake gudanar da zaÉ“en fidda gwani na takarar shugabancin kasa karkashin jam’iyyar APC na bayyana cewar, É—an takarar shugabancin kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bayyana abin da zai aiwatar da zarar ya yi nasarar lashe zabe. A cewarsa, a shirye yake da ya soma aiki daga ranar farko da ya zama shugaban Æ™asa, ba tare da É“ata wani lokaci ba domin lalubo mafita. Ya bayyana cewa shi mai É—aukar abubuwa da gaske ne kuma bai zo…

Cigaba Da Karantawa

2023: Ni Nafi Kowa Cancantar Zama Shugaban Kasa – Ahmad Lawan

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban majalisar Dattawa kuma É—an takarar Shugaban Æ™asa a karkashin jam’iyyar APC Ahmed Lawan, ya bayyana cewar shi ne ya fi kowa cancantar zama shugaban Æ™asa a shekarar zaÉ“e ta 2023. A cewarsa, ya shekara 23 a majalisa kuma a cewarsa yana da Æ™warewar da zai jagoranci Najeriya. Ya bayyana cewa ko a Æ™asashen da suka ci gaba, akwai da dama daga cikin waÉ—anda suka zama shugaban Æ™asa da Æ´an majalisa ne inda ya ce hakan ya sa ya…

Cigaba Da Karantawa

Janyewar ‘Yan Takara Ga Tinubu Alamun Nasara Ne – Ganduje

Mai girma Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa janyewar da ‘yan takara suke don mara wa Bola Ahmed Tinubu baya alamu ne cewa É—an takarar tasu zai yi nasara. Ganduje ya faÉ—i hakan ne yayin da yake tattaunawa da manema labarai a filin Eagle Sqaure, inda taron jam’iyyaer APC ke gudana yanzu haka. “Wannan alamar nasara ce kuma ka ga yadda kowa yake murna saboda É—an takararmu Bola Tinubu ya fi sauran ‘yan takara cancanta”.

Cigaba Da Karantawa

‘Yan Najeriya Ne Suka Zabi Buhari Ba Mutum Guda Ba – Fadar Shugaban Kasa Ga Tinubu

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Fadar shugaban Æ™asa ta bayyana cewa Miliyoyin ‘yan Najeriya ne suka fito Æ™wai da Æ™warÆ™warta sukazaÉ“i Buhari ya shiga ofishin shugaban Æ™asa a shekarar 2015. Babu wani mutum É—aya da zai yi ikirarin cewa shi ya taimaka wa Buhari ya zama shugaban Æ™asa a zaÉ“en 2015, a cewar fadar ta shugaban Æ™asa. Fadar shugaban Æ™asa ta yi wannan kalaman ne yayin martani ga ikirarin jagoran jam’iyyar APC na Æ™asa, Bola Ahmed Tinubu dake ikirarin shine silar zaman Buhari Shugabàn Æ™asa. A wata…

Cigaba Da Karantawa

Takarar Ahmad Lawan: Buhari Ya Yi Harshen Damo

Labarin dake shigo mana daga babban birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ba za a Æ™aÆ™aba dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa ba, za a kasa kowa ya É—auka. A cewar wata sanarwa da Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasa Buhari ya fitar, Buhari ya bayyana haka ne a ranar Litinin a wani taro da gwamnonin APC na yankin Arewa suka yi da shi. Kalaman shugaban na zuwa ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa…

Cigaba Da Karantawa

2023: APC Na Dab Da Zama Tarihi – Atiku

Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar ‘Dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce wa jam’iyya mai mulki dubunta zai cika a zaben 2023. Atiku ya ce jam’iyya mai mulki ta APC ta gaza bayyana damuwarta game da wadanda ‘yan ta’adda suka kai wa farmaki a Owo, jihar Ondo yayin da gaba daya kasar ke cikin jimami. Sannan ta gaza fasa gabatar da taro da ‘yan takarar shugaban kasarta a ranar da aka kai harin, inda ya…

Cigaba Da Karantawa