Nasarar Uba Sani Nasara Ce Ga Jama’ar Kaduna – Shehu Molash

An bayyana nasarar da zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani na jam’iyyar APC ya samu a zaɓen da ya gabata a matsayin wata nasara ce ga jama’ar jihar gaba ɗaya. Mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar Kaduna kan harkokin siyasa Alhaji Muhammad Shehu Molash ya bayyana hakan a sakon godiya da ya aike wa jama’ar Jihar Kaduna kan nasarar sabon Gwamna Malam Uba Sani. Molash wanda shine mai magana da yawun kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa na jam’iyyar APC shiyyar Arewa maso yamma, kuma mataimakin darakta na tsare-tsare…

Cigaba Da Karantawa

Ban Da Wani Shiri Na Yin Tuggu Ga Tinubu – Gwamnan Babban Banki

An ruwaito wata kafar yada labarai ta bayyana cewa babban bankin ya saki naira miliyan 500 na cikin sabbin takardun kudi domin bai wa dan takarar gwamna a jam’iyyar Labour a Legas, Mista Gbadebo Rhodes-Vivour nasara kan sauran manyan jam’iyyu biyu a zaben gwamnan da za a yi ranar Asabar mai zuwa. Amma a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, mukaddashin Daraktan Sadarwa na CBN, Isa Abdulmumin, ya ce Emefiele “bai taba ganawa ko ma magana da Mista Gbadebo Rhodes Vivour ba”. Da yake ambato wasu majiyoyi…

Cigaba Da Karantawa

Wasu Daga Cikin Ayyukan Sanata Uba Sani A Matakin Kiwon Lafiya (III)

Daga Ibrahim Ibrahim LAFIYA a ka ce uwar jiki. Sai da lafiya komai ke samuwa a rayuwa. A wannan ɓangaren Sanata Uba Sani ya yi namijin ƙoƙari domin ganin al’ummar sa sun samu sauƙi wajen neman lafiya mai inganci. Sanatan ya bi lungu da saƙo domin ganin ya inganta harkar lafiya a mazaɓun sa da kuma daukacin Jihar Kaduna baki daya. Ga kadan daga cikin wasu cibiyoyin kiwon lafiya da Sanata Uba Sani ya gina, kuma ya samar masu da kayan aiki irin na zamani; Sanata Uba Sani ya gina…

Cigaba Da Karantawa

Kaduna: Zan Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Idan Na Lashe Zabe – Ashiru Kudan

Ɗan takarar gwamnan jihar Kaduna a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar adawa ta PDP Isah Ashiru Kudan, ya bayyana hanyoyin da zai bi domin magance matsalar ƴan bindiga a jihar. Ashiru Kudan ya bayyana cewa domin shawo kan matsalar, gwamnatin sa zata tattauna da ɓata garin domin samun maslaha inda yayi nuni da cewa su ma mutane ne ba dodanni ba. Kudan ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da tashar talabijin ta ARISE TV, kan batutuwan da suka shafi nasarar jam’iyyar sa a zaɓen gwamna da na dan ƴan majalisun jihar…

Cigaba Da Karantawa

Wasu Daga Cikin Ayyukan Uba Sani A Harkar Ilimi (II)

Daga Ibrahim Ibrahim. MASU hikimar zance na cewa, da ɗan gari akan cin gari. To, Sanata Uba Sani dai kowa ya san cewa jajirtacce ne tun kafin ya tafi Majalisar Dattawa ta 9. Sanatan ya nuna cewa, lallai shi Haziki ne kuma masoyin Al’ummar da su ka tura shi zuwa kujerar da ya ke a kai yanzu. A halin da ake ciki yanzu, tun daga lokacin da ya ɗare kan kujerar sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Uba Sani ya yi manyan ayyuka na raya al’umma da ci-gaban su. A yau…

Cigaba Da Karantawa

Adalin Shugaba: ECOWAS Za Ta Gwangwaje Buhari Da Lambar Girmamawa

Yayin da ya rage saura kwanaki 83 a mulki, shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai samu lambar yabo ta Dimokuradiyya da kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka za ta gwangwaje shi da ita. Shugaban kungiyar na yankin kuma shugaban kasar Guinea Bissau Umaro Embalo ne ya bayyana hakan a taron kasashen biyu da suka yi da Buhari a gefen taron majalisar dinkin duniya kan kasashen da suka fi ci gaba a birnin Doha na kasar Qatar. “Buhari za a sanya sunansa a cikin jerin sunayen karramawa a sabon ginin hedkwatar…

Cigaba Da Karantawa

Yadda Siyasar Jihar Kaduna Ta Koma Ta Addini Da Kabilanci

Yayin da jam’iyyu ke shirin tunkarar zaben gwamna dana ‘yan majalisun dokokin jihohi a Najeriya, wani batu da ke fitowa fili a fagen siyasar jihar Kaduna shi ne na siyasar addini da kuma ƙabilanci. A baya dai jihar ta sha fama da rikice-rikice masu nasaba da addini da kabilanci, lamarin da masana ke nan suka ce yana matukar janyo komawa baya ga tsarin dimmkradiyya. Duk da cewa akwai masu neman takarar kujerar gwamna a jihar fiye da 10, takarar tafi zafi ne a tsakanin jam’iyyar APC da kuma PDP.Masana harkokin…

Cigaba Da Karantawa

Dalilin INEC Na Cire Sunan Ado Doguwa Daga Jerin Zababbun ‘Yan Majalisa

A ranar Larabar da ta gabata ne wata kotun Magistira a Kano ta tisa keyar shugaban masu rinjayen na majalisar tarayya zuwa gidan gyara hali. Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta cire sunan shugaban masu rinjaye a majalisar wakila wanda yake cikin wani rikici Alhassan Ado Doguwa daga jerin sunayen wakilan da suka yi nasara a zaben da ya gabata.Wannan mataki na hukumar ya faru bayan da INEC ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan…

Cigaba Da Karantawa

Kano: INEC Ta Cire Sunan Ado Doguwa Daga Jerin Zababbun ‘Yan Majalisa

Hukumar zaɓe ta ƙasa ta cire sunan shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya Alhassan Ado Doguwa daga cikin jerin sunayen zaɓaɓɓeun ‘yan majalisar wakilan ƙasar da suka yi nasara a zaɓen da aka gudanar cikin watan Fabrairu. Hukumar zaɓen ƙasar ce dai tun da farko ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen ɗan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazaɓar Doguwa da Tudunwada a jihar Kano da ke arewacin Najeriya. Jami’in tattara sakamakon zaɓen Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya bayyana cewa Doguwa na jam’iyyar APC…

Cigaba Da Karantawa

Kano: INEC Ta Cire Sunan Ado Doguwa Daga Jerin Zababbun ‘Yan Majalisa

Hukumar zaɓe ta ƙasa ta cire sunan shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya Alhassan Ado Doguwa daga cikin jerin sunayen zaɓaɓɓeun ‘yan majalisar wakilan ƙasar da suka yi nasara a zaɓen da aka gudanar cikin watan Fabrairu. Hukumar zaɓen ƙasar ce dai tun da farko ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen ɗan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazaɓar Doguwa da Tudunwada a jihar Kano da ke arewacin Najeriya. Jami’in tattara sakamakon zaɓen Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya bayyana cewa Doguwa na jam’iyyar APC…

Cigaba Da Karantawa

Kaduna: Zabar PDP Asarar Kuri’a Ne – Hunkuyi Dan Takarar Gwamna A NNPP

Dantakarar Gwamnan Jihar Kaduna a inuwar jam’iyyar NNPP Sanata Suleiman Hunkuyi ya janyo hankalin Jama’ar Jihar Kaduna da su guji jefa kuri’unsu wajen Dan takarar da suka san ba zai yi nasara ba, su guji yin zaben tumundare, a ranar 11 ga watan Maris. Sanata Suleiman Hunkuyi ya bayyana haka ne a ranar Juma’a, yayin da yake zantawa da manema labarai domin janyo hankalin Al’ummar Jihar Kaduna akan su guji zaben tumundare, kar su yarda su jefa kuri’unsu ga Dan takarar da kowa ya shaida cewa bai da cancanta. Sanata…

Cigaba Da Karantawa

Zaben Gwamna: Bamu Da Dan Takara Sai Uba Sani – Malaman Kaduna

Rahotannin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar Malaman Addinin Musulunci yau a hudubobin su na juma’a sunce basu da ɗan takarar gwamna a Jihar sai Sanata Uba Sani na jam’iyya mai Mulki a zaɓen dake tafe. “Mu a Jihar Kaduna Uba Sani za mu yi, mu dubi gaba mu yafe ma Gwamnati koda anyi mana ba daidai ba. Don haka muyi Malam Uba Sani da zuciya ‘daya mu rakashi da addu’a. A yayin hudubar saMalam Khamis Amisry, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Natatu dake kan titin byepass…

Cigaba Da Karantawa

Dalilan Cancantar Sanata Uba Sani A Gwamnan Jihar Kaduna (1)

Daga Ibrahim Ibrahim ƊAN takarar zama gwamnan Jihar Kaduna a jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani jajirtacce ne a wurin gudanar da aiki, taimakon jama’a, kawo ci-gaba ga al’umma tun kafin ya samu damar zama sanatan Kaduna ta tsakiya. Sanata Uba Sani mutum ne da ya kasance mai tausayin al’umma, wanda duk inda ya yi aiki sai da ya aje abin a yaba masa tare da jinjina. Kamar yadda kowa ya sani Sanata Uba Sani ya taka rawar gani a tsawon shekaru huɗu da ya yi a matsayin sanatan Kaduna ta…

Cigaba Da Karantawa

Na Yaba ‘Yan Najeriya Bisa Zabar Tinubu Da Suka Yi – Aisha Buhari

Uwargidan shugaban ƙasa Aisha Buhari, ta yaba ‘yan Najeriya bisa zabar Tìnubu da suka yi sannan ta nuna ƙwarin guiwar da ta ke da shi kan zaɓaɓɓen shugaban ƙasar nan, Bola Tinubu. Aisha Buhari ta nuna ƙwarin guiwa kan cewa Bola Tinubu yana da cikakkiyar ƙwarewar da zai kawo haɗin kai, zaman lafiya da cigaba a ƙasar nan. A saƙon taya murna da uwargidan shugaban ƙasar ta sanya wa hannu sannan ta sanya a shafinta na Facebook, ranar Laraba, 1 ga watan Maris a Abuja, ta nuna fatan cewa Tinubu…

Cigaba Da Karantawa

2023: Akwai Kura-Kurai A Zaben Da INEC Ta Gudanar – NNPP

Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) mai kayan marmari tayi kira da a soke sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na 2023. Jam’iyyar tayi wannan kiran ne a wani taron manema labarai da shugaban ta na ƙasa, Rufai Alkali, yayi a birnin tarayya Abuja. Alkali yace yadda INEC ta gudanar da zaɓen shugaban ƙasar, hukumar ta mayar da ƙasar nan baya wajen yin irin zaɓukan da akeyi kafin shekarar 2015. “Mun damu matuƙa kan abubuwan da suka faru ranar zaɓe, hukumar…

Cigaba Da Karantawa

Kungiyar Afenifere Ta Yi Tir Da Zaben Tinubu

Pa Ayo Adebanjo, shugaban kungiyar Yarabawa ta Afenifere, ya mayar da martani kan ayyana ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa. Yayin da yake magana a wata tattaunawa ta wayar tarho da BBC, Adebanjo ya bayyana zaɓen da ya bai wa Tinubu nasara a matsayin mai cike da kura-kurai. Ya ce sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba abu ne da za a amince da shi ba, kuma hakan na iya haifar rikici a ƙasar. Adebanjo ya ce gazawar da INEC…

Cigaba Da Karantawa

Za Mu Kalubalanci Nasarar Tinubu A Kotu – Jam’iyyar Labour

Jam’iyyar Labour Party (LP) mai adawa a zaɓen shugaban ƙasa na Najeriya ta bayyana cewa za ta ƙalubalanci sakamakon zaɓen da ya bayyana Bola Tinubu na jam’iyyar APC mai mulki a matsayin wanda ya yi nasara. Yayin da yake jawabi a Abuja a yau Laraba, ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam’iyyar LP, Datti Baba Ahmed, ya jaddada cewa akwai kura-kurai a zaɓen. “Mun shiga zaɓen a matsayin LP kuma mun yi nasara da sunan LP,” a cewarsa. “Kuma za mu ƙwaci haƙƙinmu da sunan LP”. Tun a ranar Talata…

Cigaba Da Karantawa

Babu Gaskiya A Zaben Shugaban Kasa Da Aka Yi A Najeriya – Amurka

Wakilin Ƙasar Amurka, Ambasada Green, ya ce tsarin zaɓen shugaban ƙasa da INEC ta shirya babu gaskiya a cikin sa ko misƙala zarra. Green ya faɗi haka ne a lokacin da yake zantawa da tashar talabijin ta Arise Tv a Babban Birnin Tarayya Abuja. Ya kuma ƙara da cewa INEC ta kunyata Najeriya da nahiyar Afrika baki daya. Sahihancin sakamakon su ba abin dogaro ba ne sam, Inji shi. Ina mai nuna baƙin ciki na tare da duk yawan biliyoyin kasafin kudin wannan zabe da a ka kashe amma babu…

Cigaba Da Karantawa

Shugabancin Kasa: Tinubu Ya Lashe Zabe A Jihar Ekiti

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar jam’iyya mai mulki ta APC, wadda ke marawa Bola Tinubu baya ta lashe zaben jihar Ekiti da yawan kuri’u 201,494, sai Atiku Abubakar na PDP da ya samu yawan kuri’u 89,554, inda jam’iyyar Labour ta Peter Obi ta zo na uku da kuri’u 11,397, yayin da NNPP Rabi’u Musa Kwankwaso ta samu kuri’u 264. Haka zalika, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya lashe zaben shugaban kasa a jihar Osun. Atiku ya samu nasara a kananan…

Cigaba Da Karantawa

Zaben Shugaban Kasa: INEC Ke Da Alhakin Sanar Da Sakamakon Zabe – Yakubu

Hukumar zaɓe ta ƙasa ta gargaɗi jam’iyyun siyasa kan yaɗa sakamakon zaben shugaban ƙasar da na ‘yan majalisun dokoki na tarayya. Shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a lokacin ƙaddamar da buɗe zauren tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a Abuja babban birnin ƙasar. Farfesa Mahmood ya ce hukumar INEC ce kawai doka ta ɗora wa alhakin fitar da sakamakon zaɓen. “Ina kira ga jam’iyyun siyasa da kafofin yaɗa labarai da su ɗauki alkaluman sakamakon daga sakamakon da muka sanar, a matsayinmu na waɗanda doka ta ɗora wa…

Cigaba Da Karantawa