Akwai Gyara A Harkar ‘Yan Kannywood – Adam Zango

Shahararren dan wasan Hausa fim na masana’atar Kannywood Adam Zango ya bayyana cewar da akwai gyara a yadda harkar ta su ke tafiya a halin yanzu da ya kamata a ɗauki matakin gyara. Adam Zango na bayani ne a yayin mayar da martani dangane da sukar da malaman addini da sauran jama’a ke yi musu na bata tarbiyya maimakon gyaranta. Jarumin ya ce tabbas idan har ɓera da sata babu shakka daddawa ma ta wari, yadda harkar ‘yan fim ke tafiya a yanzu abin takaici ne, an kai ga matsayin…

Cigaba Da Karantawa

Fina-Finai: Marigayi Ibiro Ya Cika Shekaru Takwas Da Rasuwa

An haifi marigayi Rabilu Musa Ibro a shekarar 1971. Ya yi karatun Firamare dinsa a Danlasan da ke cikin karamar hukumar Warawa. Sannan kuma ya yi Sakandare a Kwalejin horon malamai ta Wudil (Teachers College). Daga nan ne ya shiga aikin gidan Yari (Prison Service) a shekarar 1991. Ya yi shekara takwas Ya na aikin Gandiroba inda ya kai matakin insfekto, daga nan ne ya bari ya cigaba da sana’ar wasan kwaikwayo. Rabilu Musa Ibro ya fara sana’ar Fim a tun ya na aji uku na makarantar sakandare. Ya na…

Cigaba Da Karantawa

Duniyar Fina-Finai: Jaruma Halima Atete Za Ta Amarce

Labarin dake shigo mana daga jihar Kano na bayyana cewar fitacciyar Jarumar Kannywood Hajiya Halima Atete za ta amarce a Kwanan nan. Tauraruwar Kannywood Halima Yusuf Atete za ta amarce da angonta Mohammed Mohammed Kala wadanda za a daura aurensu ranar Asabar 26 ga watan Nuwamban 2022 a Maiduguri. A ‘yan lokutan nan dai ana yawan samun yin aure na Jaruman Kannywood lamarin da jama’a ke gani wata alama ce da Jaruman na Kannywood musamman Mata za su yi bankwana da Masana’antar zuwa gidan Aure.

Cigaba Da Karantawa

Fina-Finai: Ina Nan Da Raina Ban Mutu Ba – Kamaye

A safiyar ranar jiya ne wani labari ya karade shafukan sada zumunta ana fadin cewa Allah yayiwa fitaccen Marubucin nan kuma darakta haka kuma a lokaci daya jarumi a masana’antar kannywood Dan Azumi Baba wanda akafi sani da Kamaye rasuwa. Jaruman Kannywood da dama sun wallafa hakan,wasun su sun karyata kansu daga baya,yayin da wasu kuma suka cire wallafar ba tare da bada wani ba’asi ba. Bayan mun gudanar da bincike ne muka tabbatar muku da cewa yana nan a raye cikin koshin Lafiya. Haka kuma shima jarumin da kansa…

Cigaba Da Karantawa

Dalilina Na Daina Rubuta Shirin Fim Din Labarina – Birniwa

Shahararren marubucin fina-finan Kannywood Ibrahim Birniwa ya ce ya daina rubuta fitaccen fim ɗin Labarina mai dogon zango saboda rashin jituwa tsakaninsa da masu shirya shi da kuma aiki kan nasa fim ɗin. Duk da cewa rashin jituwa ce ta sa marubucin ya fita daga fim ɗin, sai dai ya ƙi faɗa wa BBC Hausa ainahin abin da ya faru, yana mai cewa “da ni nake rubuta fim ɗin da zuwa yanzu ya zo ƙarshe”. Da yake magana ta cikin shirin Amsoshin Takardunku na Sashen Hausa na BBC a ƙarshen…

Cigaba Da Karantawa

Kano: Tinubu Ya Gwangaje Kannywood Da Kyautar Miliyan 50

Labarin dake shigo mana daga jihar Kano na bayyana cewar Bola Ahmed Tinubu, ‘dan takarar kujerar shugabancin kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 ya gwangwaje masana’antar Kannywood da gudumawar N50 miliyan domin cigaban masana’antar. Mujallar fim ta ruwaito cewa, Tinubu ya bayar da wannan makudan kudaden ne a yayin da ya halarci taro na musamman da ‘yan fim suka hada masa a daren Lahadi a fadar gwamnatin jihar Kano. A yayin jawabi kan manufar taron, Furodusa Abdul Amart Maikwashewa ya ce: “Wannan taron na matasan fim ne masu goyon…

Cigaba Da Karantawa

Dalilin Da Ya Sa Nake Tikar Rawa Da Waka A Gidan Gala – Tahir Fagge

Shahararren Dan wasan kwaikwayo Mai Suna Alhaji Tahir Fagge ya Bayyana cewa Dole Ce ta Sanya shi fitowa a cikin wata Waka da aka Ganshi Yana taka rawa da wata yarinya awajen Wani Gala. Tahir Fagge yace ya shiga mawuyacin Hali sakamakon jarrabawa da Allah yayi Masa na Rayuwar Sa. “Yace ya kasance Cikin mawuyacin hali Kuma Babu yadda zaiyi sakamakon yadda wasu Mutane suka Gaza fahimtar halin da yake ciki na rashin lafiya. “Bani da kudin da Ake bukata a ASibiti Kuma sau dadama wasu mutane basa iya taimakon…

Cigaba Da Karantawa

Kano: Kotu Ta Bada Umarnin Kama Mawaki Ado Gwanja

Labarin dake shigo mana daga jihar Kano na bayyana cewar wata kotun shari’a ta umurci hukumar yan sanda ta damke sanannen mawaƙi Ado Gwanja da wasu mutum 10 kuma ta bincikesu kan koyawa matasa rashin tarbiyya a kafafen ra’ayi da sada zumunta, wani jami’in kotun ya bayyanawa AFP ranar Alhamis. Kotun ta bada umurnin ne tun ranar Talatar makon jiya bayan lauyoyi sun shigar da kara inda suka bukaci hukunta Ado Gwanja da ire-irensa bisa wakokin rashin tarbiyya da daurawa a yanar gizo, jami’in kotun Baba-Jibo Ibrahim ya bayyana hakan.…

Cigaba Da Karantawa

Har Yanzu Ban Samu Namijin Da Ya Yi Mini Ba – Jarumar Fina-Finai

Fitacciyar jarumar masana’antar Nollywood, Bimbo Akinsanya wacce aurenta ya mutu lokacin tana da yaro mai wata uku a shekarun baya da suka gabata, tace ta mayar da hankali kan fim a yanzu fiye da batun aure. A tattaunawarta da jaridar Vanguard, tace tana kokarin ganin ta ba wa ‘danta lokacinta wanda hakan ke da matukar muhimmanci. Tantancewa nake yi, har yanzu ban ga nagartaccen namijin da ya dace da ni ba, ta bayyana yadda take kula da ‘danta ita kadai ba tare da tallafin uban yaron ba. “Ba abun wasa…

Cigaba Da Karantawa

An Gurfanar Da Jaruma Hadiza Gabon A Kotun Shari’a Ta Kaduna

Labarin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewar Fitacciyar jarumar Kannywood, Hadiza Gabon, ta musanta sanin ma’aikacin nan ɗan shekara 48, Bala Musa, wanda ya yi ikirarin ta masa alƙawarin aure. Jarumar wacce ta bayyana a gaban Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Magajin Gari Kaduna ranar Talata, ta faɗa wa Kotun cewa ba ta san mutumin da ake magana a kan shi ba. Da take jawabi ta bakin lauyanta, Barista Mubarak Sani Jibril, a harabar Kotun, Gabon ta musanta tuhumar da ake mata baki ɗaya inda…

Cigaba Da Karantawa

Magidanci Ya Maka Hadiza Gabon Kotu Saboda Kin Aurensa

Wani maigidanci mai kimanin shekara 48 ya maka jarumar fina-finan Hausa na Kannywood, Hadiza Gabon, a gaban wata kotun shari’ar Musulunci da ke Kaduna saboda ta ki amincewa ta aure shi. Maigidancin, mai suna Bala Musa, wanda ma’aikacin gwamnati ne ya shaida wa kotun cewa sun jima suna soyayya da jarumar, bisa alkawarin za ta aure shi, amma ta ci gaba da yaudarar shi. Bala ya ce, “Ya zuwa yanzu, na kashe mata N396,000. Duk lokacin da ta tambaye ni kudi na kan kashe mata ba bata lokaci cikin fatan…

Cigaba Da Karantawa

Fina-Finai: Gwamnatin Kaduna Za Ta Gina Fim Village

Labarin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewar babban sakataren hukumar KADIPA na jihar Kaduna, Khalil Nur Khalil ya cigaba da kokarin ganin an gina kauyen shirya wasan kwaikwayo wato’Fim Village’. A wani jawabi da ya fito daga shafin KADIPA a dandalin Twitter a ranar Alhamis, an fahimci gwamnatin Kaduna tana nan a kan aikin ‘Film Village’ domin bunkasa rayuwar matasa. Khalil Nur Khalil ya hadu da wakilan KCTA, shugabar Fasaha Café, Joseph Ike, da fitacciyar ‘yar wasar kwaikwayo, Rahma Sadau a kan wannan shirin. Shugaban na KADIPA…

Cigaba Da Karantawa

Na Yi Nadamar Shiga Rikicin Zango Da Ali Nuhu – BMB

Jarumin fina-finan Hausa, wanda furodusa ne kuma darakta, Bello Muhammad Bello, wanda aka fi sani da BMB, ya bayyana shirinsa na dawowa sana’ar fim da sauran abubuwa dangane da rayuwarsa ta ilimantarwa. A tattaunawar da Daily Trust ta yi da BMB, ya fara da gabatar da kansa inda ya ce: “Sunana Bello Muhammad Bello, an fi sani da General BMB. Ni furodusa ne, darekta ne, jarumi sannan mai rubuta labari kuma na tashi ne a cikin rayuwar musulunci a cikin garin Jos da ke Jihar Filato. Kuma na yi makarantar…

Cigaba Da Karantawa

‘Ya’yan Sarkin Kano Na Neman Rayuwata – Tsohuwar Jarumar Kannywood

Tsohuwar jarumar Kannywood, wadda aka fi sani da sunan Maijidda Ibrahim, na neman agajin ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan’adam da sauran jama’a kan halin ha’ula’in da ta ke ciki Lokacin da ta ke fitacciyar jaruma a masana’antar finafinai ta Kannywood, sunan ta Maijidda Ibrahim, yanzu kuma Hajiya Hauwa Bello Ado Bayero. Ta na ɗaya daga cikin ɗimbin mata ‘yan fim da su ka yi aure kuma su na zaune a gidan miji. Tsawon shekaru 21 kenan tun da tsohuwar jarumar, wadda aka fi sani da sunan Maijidda Khusufi saboda wani fitaccen…

Cigaba Da Karantawa

Mutuwa Ta Dauke Jarumar Kudanci A Coci

Labarin dake shigo mana daga Jihar Enugu na bayyana cewar Likitoci a asibitin East Side a Jihar Enugu sun tabbatar da mutuwar jarumar fina-fina ta Nollywood, Chinedu Bernard. Ta yanke jiki ta fadi ne a yayin da ta ke aikin tsaftace coci na St. Leo the Great Catholic Church da ke rukunin gidajen Tarayya a jihar. Faston cocin, Rabaran Fada Uchendu Chukwuma, da wasu masu ibada a cocin, sun garzaya da ita asibitin a inda aka tabbatar ta rasu. A cewar wani rubutu da daya daga cikin masu aiki a…

Cigaba Da Karantawa

Jaruma Ummi Rahab Za Ta Amarce

Labarin dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewar manuniya tana nuna cewa jarumi kuma mawaki sannan mai daukar nauyin fim din Wuff mai dogon zango ya na gab da auren jarumar da ke haska fim din, Ummi Rahab. A makon da ya gabata rade-radin ya karu bayan jarumar ta wallafa hoton Lilin Baba a shafinta na Instagram, inda ta kira shi da “Masoyinta kuma mijinta kuma Aljannarta.” A karkashin rubutun na ta kamar yadda Aminiya ta nuna, mutane sun dinga tsokaci iri-iri har Ali Artwork yana cewa: “Insha…

Cigaba Da Karantawa

Almajiranci: Fati Slow Ta Goyi Bayan Sarkin Waƙa

Tsohuwar jarumar Kannywood, Fati Usman da aka fi sani da Fati Slow ta fito ta goyi bayan caccakar abokiyar sana’arsu, Nafisa Abdullahi da Naziru Ahmad ya yi kan zagin iyayen da ke tura ‘ya’yansu almajiranci. Fati Slow ta ce tabbass babu asararre sama da mutumin da zai dunga iskanci yana watsawa duniya ana zagin iyayensa amma ko a jikinsa. A wani bidiyo da ta saki a shafinta na Instagram inda a ciki ne ta yi shagube ga Nafisa, ta bayyana cewa jarumar bata da ilimin addini shi yasa har take…

Cigaba Da Karantawa

Ina Kan Ra’ayina Na Sukar Masu Tura ‘Ya’ya Almajiranci – Nafisa Abdullahi

A rubutu da tayi a shafinta na Twitter mai suna @NafisatOfficial, ta ce: “Ya bayyana cewa wasu mutanen ba su ji dadin maganar da nayi ba, na cewa a daina haihuwar ‘ya’yan da ba za a iya daukar nauyinsu ba. Eh, na san an ce ku yi aure ku hayayyafa, amma a ina aka ce ku haifa ‘ya’yan ku watsar da su?. “Kun cika son bada kariya ga abunda kuka san cewa ba daidai bane. Suna cewa wai in bari in yi aure kafin in tsoma bakina a cikin irin…

Cigaba Da Karantawa

A Kasuwa Nake Ga Duk Mai Bukata – Momi Gombe

Shahararriyar Jarumar Finafinan Hausa Maimuna Abubakar wadda aka fi sani da suna Momi Gombe ta bayyana cewar a halin yanzu ba tada da wani buri wanda ya wuce yin aure da raya sunnar ma’aiki. Momi Gombe ta bayyana hakan ne a yayin wata tattaunawa da gidan Rediyon BBC Hausa ya yi da ita cikin shirin “Daga Bakin Mai Ita”. A cewar Jarumar tabbas ta taɓa yin aure ita Bazawara ce amma ba ta haihu, a halin yanzu a kasuwa nake ga dukkanin mai bukatar aure. Sai dai Jarumar ta ƙaryata…

Cigaba Da Karantawa

Jarumin Wasan Barkwanci Ya Yi Gargaɗin Sa Matan Da Aurensu Ya Mutu A Fim

Furodusa kuma mai wasan barkwanci na masana’antar Kannywood, Malam Habu wanda aka fi sani da Mazaje, ya yi kira da a daina sa duk wata jarumar masana’antar da ta yi aure, sannan aurenta ya mutu ta dawo masana’antar. A wani dan karamin bidiyo da ya fitar, Mazaje ya ce, “duk wani furodusa ya sake wata ta fito a aure ya saka ta a fim, ni babu abin da zan ce masa, sai wuta balbal.” Sannan ya rubuta a saman bidiyon cewa, “duk wata jarumar Kannywood da ta yiaure ta fito…

Cigaba Da Karantawa