Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce Najeriya ce ta fi dacewa da ƙasar da masu zuba hannun jari daga Amurka za su zuba kudadensu. Shugaban ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a Washington DC yayin da yake wata tattaunawa ta musamman ta kasuwanci tsakanin Amurka da Najeriya da kuma zauren masu zuba hannun jari, a wani taro da kungiyar hadinkan Amurka da Afrika ta shirya tare da hadin gwiwar ma’aikatar kasuwanci da zuba jari, a gefen taron shugabannin Afrika da Amurka. Yace baya ga yawan da kasar ke da…
Cigaba Da KarantawaCategory: Babban Labari
Babban Labari
Shekaru Masu Albarka: Buhari Ya Cika Shekaru 80 A Duniya
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana mana cewar a Asabar ne 17 ga watan Disamban shekara ta 2022 shugaban kasa Muhammadu Buhari ya cika shekara 80 da haihuwa. An haifi shugaba Buhari ne a ranar 17 ga watan Disamba a garin Daura na masarautar Daura da ke Jihar Katsina. Tuni manyan mutane Sarakuna, Malamai da ‘yan siyasa suka soma tura sakon taya murna ga shugaban kasar. Cikin wadanda suka soma aike sakon murnarsu ga shugaban akwai dan takarar shugabanci kasa a inuwar Jam’iyyar APC, Bola Ahmed…
Cigaba Da KarantawaKalaman Batanci: Kotu Ta Yanke Wa Sheikh Abduljabbar Hukuncin Kisa
Babbar Kotun Shari’ar Musulunci ta Jihar Kano ta yanke wa Sheikh Abduljabar Nasiru Kabara hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan samun sa da laifi yin kalaman rashin tarbiyya ga Annabi Muhammad SAW. An yanke hukuncin ne a ranar Alhamis bayan da Mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola ya ce an same shi da dukkan laifi huɗu da ake tuhumar sa da su. Mai Shari’a Sarki Yola ya ce malamin yana da kwana 30 don ɗaukaka ƙara idan bai gamsu da hukuncin ba. Cikin iƙirarin da Abduljabbar ya yi a wa’azizzikan da…
Cigaba Da KarantawaNa Yi Dukkanin Abin Da Zan Iya A Shugabancin Najeriya – Buhari
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar mai girma Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce ya yi iya bakin kokarinsa a matsayinsa na shugaban Najeriya. Shugaban ya shaida hakan ne a Amurka lokacin da yake tarban Sakatare Janar na kungiyar Abu Dhabi, Sheikh Al- Mahfoudh Bin Bayyah da mataimakinsa, Fasto Bob Roberts na Amurka, a wata ziyarar da suka kai masa. Buhari ya ce Najeriya kasa ce mai yawan al’umma da ke fuskantar kalubale daban-daban, sai dai a tsawon shekarun mulkinsa ya san cewa ya yi…
Cigaba Da KarantawaZan Gina Sabuwar Najeriya Idan Na Zama Shugaban Kasa – Tinubu
Rahotannin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar ɗan takarar Kujerar zama shugaban kasa a inuwar jam’iyya mai mulki ta APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, yace da ikon Allah ‘yan Najeriya ba zasu yi da nasani ba idan suka zaɓe shi shugaban kasa a 2023. Tinubu ya ba da wannan tabbacin ne a wurin gangamin yakin neman zaɓensa da ya gudana a Kaduna ranar jiya Talata. Gangamin Kaduna somin taɓi ne na fara yakin neman zaben shugaban kasa na APC a shiyya mafi yawan kuri’u a Najeriya watau…
Cigaba Da KarantawaBoko Haram: Karya Ce Babu Inda ‘Yan Ta’adda Za Su Boye A Sambisa – Atiku
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar ɗan takarar shugabancin ƙasa a babbar jam’iyya adawa ta PDP Atiku Abubakar, yace duk ƙarya ce ake yi kawai, amma babu wani surƙuƙin dajin da ‘yan ta’adda za su iya ɓoyewa a Dajin Sambisa, a ce wai an kasa gano inda su ke. Atiku ya ce ya shiga dajin, amma babu komai daga ciyayi, sai kalage da gezoji kawai. Ya ce kan sa na ɗaurewa ganin yadda ake ta gaganiya da Boko Haram, amma an kasa ganin bayan su…
Cigaba Da KarantawaBuhari Bai Da Masaniya Kan Kwamitin Da Gudaji Ke Ikirarin Shugabanta – Garba Shehu
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan wani ikirari da kwamiti na musamman da shugaban kasar ya kafa domin ya gudunar da bincike a kan cajin cirewa da ajiyar kudi a asusun banki ƙarƙashin jagorancin Honorabul Gudaji Kazaure. Shugaban kwamitin, Gudaji Kazaure ya yi zargin cewa wasu hukumomin da binciken ya shafa suna kokarin hana ruwa gudu game da aikin nasa, da kuma hana shi ya mika wa shugaba Muhammadu Buhari rahotonsa. A cewar kwamitin wanda aka dora…
Cigaba Da KarantawaBuhari Zai Tafi Amurka Halartar Taron Shugabannin Afirka A Yau
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban kasaMuhammadu Buhari a yau Lahadi zai tafi Amurka domin halartar taron shugabannin ƙasashen Afirka da Amurka za ta karbi bakunci. A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban kan kafofin yada labarai, Malam Garba Shehu ya fitar yau Asabar, ya ce taron wanda za a gudanar daga ranar 13 zuwa 15 ga watan Disamba da shugaba Biden zai jagoranta, na da zimmar ganin ta yi aiki da gwamnatocin Afirka da kuma al’ummomin su da ke zama…
Cigaba Da KarantawaSakon Tallafin Tinubu Na Raba Kudi Ga ‘Yan Najeriya Ba Gaskiya Ba Ne – Kwamitin Neman Zabe
Wata sanarwa da tawagar yaƙin neman zaɓen Tinubu ta fitar ta ce saƙon da ake yaɗawa na ƙarya ne kuma ba daga wurinsu ya fito ba. “Muna tabbatar da wannan saƙon na ƙarya ne saboda ba daga wajenmu ya fito ba,” a cewar Festus Keyamo kakakin tawagar kamfe ɗin Tinubu/Shettima kuma Ƙaramin Ministan Ƙwadago na Najeriya. Mista Keyamo ya zargi jam’iyyun adawa da “yunƙurin tura saƙonni marasa kan-gado da zimmar samun ƙuri’un ‘yan Najeriya”. A ranar Laraba Bola Tinubu ya faɗa wa BBC cikin wata hira cewa tabbas shi mai kuɗi…
Cigaba Da KarantawaZaben Najeriya: Ba Ma Goyon Bayan Kowa Cikin ‘Yan Takara – Birtaniya
Wakiliyar Birtaniya a Nijeriya, Catriona Liang, ce ta bayyana hakan a yau Laraba bayan wata ganawar sirri da ta yi da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC na kasa, NWC, a Abuja. Liang ta yi nuni da cewa, UK za ta yi aiki da duk wani dan takarar da ya lashe zaɓe, inda ta bayyana amincewa da dimokuradiyyar Nijeriya da kuma kudurin shugaban kasar na yin zaɓe cikin kwanciyar hankali kuma ingantacce. Ta ce: “Wannan taro ɗaya ne da na ke yi da jam’iyyun siyasa, da ƴan takarar shugaban kasa, da…
Cigaba Da KarantawaNajeriya Za Ta Cimma Burin Fitar Da Adadin Man Fetur A Kasuwannin Duniya
Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Ƙaramin ministan man fetur Timipre Sylva ya sanar da cewa zuwa mayun shekara mai zuwa, Najeriya za ta cimma burin Kungiyar Kasashen Duniya masu azrikin man fetur OPEC domin fitar da gangar mai miliyan daya da dubu dari takwas. Wata sanarwa da mai ba ministan shawara kan harkokin yaɗa labarai Horatius Egua ya fitar, ministan ya ce Najeriya za ta yi iya kokarinta domin ƙara tsaurara tsaro kan manyan hanyoyin da bututun mai na ƙasar suke da kuma toshe…
Cigaba Da KarantawaBa Dole Bane Tinubu Ya Rinka Halartar Zaman Mahawara – APC
A cikin wata sanarwa da Kwamitin yakin neman zaben Tinubu ya fitar ya ce kundin tsarin mulkin Nijeriya bai wajabtawa dan takararta halartan muhawarar da wata kungiya ta shirya ba, saboda haka ba dole bane. A wata sanarwa da Arise TV ta fitar kwanan nan ta bukaci dukkan ‘yan takarar da su mutunta kundin tsarin mulkin kasar kuma su halarci muhawarar da ta shirya. “Muna tsammanin duk ‘yan takarar da ke neman zabe kuma su kafa gwamnati a karkashin wannan tsarin mulki, ya kamata su mutunta doka, tare da halartar…
Cigaba Da KarantawaBuhari Ya Dora Tubalin Ginin Sabuwar Hedikwatar ECOWAS A Abuja
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da tubalin ginin sabuwar hedikwatar Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas a Abuja babban birnin tarayya. Shugabannin ƙasashen Guinea Bissau Umaro Embaló, da na Saliyo Julius Maada Bio, da Shugaban Ecowas Omar Alieu Touray, da Jakadan China a Najeriya Cui Jianchun, su ne suka taya Buhari saka ɗambar ginin a ranar Lahadi. Ana sa ran kammala sabuwar hedikwatsar a shekara ta 2025. Shugaba Muhammadu Buhari ya ayyana cewa hamshaƙin ginin,…
Cigaba Da KarantawaBa Mu Da Hannu A Jefa ‘Yan Najeriya Cikin Talauci – Gwamnoni
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnonin Najeriya 36 sun ce sun yi mamakin yadda ƙaramin Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-Tsare na ƙasar, Clem Agba ya zarge su da jefa Najeriya cikin talauci. A watan Nuwamba ne Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce mutum miliyan 130 ne a ƙasar ke fama da talauci, kusan kashi 63 cikin 100 na a’umar ƙasar. To sai dai a wata sanarwa da ƙungiyar gwamnonin ƙasar suka fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaran ƙungiyar Abdulrazaque Bello-Barkindo, ta…
Cigaba Da KarantawaAisha Buhari Ta Janye Karar Da Ta Kai Amìnu Muhammad
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar uwargidan shugaban ƙasa, Aisha Buhari ta janye karar da ta shigar da Aminu Muhammad a kotu. Uwargidan shugaban na neman kotu ta bi mata kadinta ne kan kalaman bata suna da take zargin Muhammad ya wallafa a kanta a shafinsa na sada zumunta. A watannin baya, Muhammad ya wallafa wani sakon Twitter da ke cewa, “mama an ci kudin talakawa an koshi,” hade da hotonta. Hakan ya sa a ranar 18 ga watan Nuwamba, jami’an tsaro suka kama Muhammad,…
Cigaba Da KarantawaBuhari Ya Kafa Tarihi Na Shugaban Da Aka Fi Zubar Da Jini A Mulkinsa – Birtaniya
A yayin da ake shirin tunkarar babban zaɓen a watannin farkon shekara mai zuwa lokaci yana kurewa wajen tabbatar da an yi zaɓen lami lafiya kuma da inganci, a cewar wani rahoto da cibiyar Tony Blair dake Birtaniya ta fitar. Cibiyar ta Burtaniya ta yi tsokaci kan irin barazanar da zaɓen ke fuskanta kan irin yadda zaɓen zai iya samun cikas daga rikicin Boko Haram, da masu fafutukar a-ware ta haramtacciyar ƙungiyar IPOB. Akwai kuma kungiyoyin ‘yan bindiga da ‘yan bangar siyasa da kuma masu yaɗa labaran karya a shafukan…
Cigaba Da KarantawaDa Dumi-Dumi: Kotu Ta Bada Umarnin Kama Shugaban Rundunar Soji
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar wata babbar kotun tarayya da ke zama a Minna, jihar Neja, ta bayar da umurnin kama babban hafsan sojin kasa Janar Faruk Yahaya bisa laifin rashin grimama kotu. Mai shari’a Halima Abdulmalik, wadda ta yanke hukuncin ta kuma bukaci da a kulle Janar Yahaya a gidan gyara hali na Minna saboda saba ma wani umurnin kotu na ranar 12 ga watan Oktoba, 2022. Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan da wata babbar kotun da ke zamn ta a…
Cigaba Da KarantawaGwamnoni Ne Suka Jefa ‘Yan Najeriya Cikin Talauci – Fadar Shugaban Kasa
Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta dora alhakin katutun talaucin da ke damun Najeriya kan gwamnonin jihohi. Karamin Ministan Kasafin Kudi da Tsare-Tsare, Clem Agba ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya ranar Laraba, kamar yadda gidan talbijin na Channels TV ya rawaito. Ya ce shirin gwamnatin tarayya na kyautata rayuwar ‘yan kasar bai yi tasirin da ya kamata ba ne saboda gwamnonin jihohi ba su bai wa gwamnatin tarayya hadin kai ba.…
Cigaba Da KarantawaKiran Gaggawa: Makaman Rasha Da Ukraine Na Kwararowa Tafkin Chadi – Buhari
Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewar ana karkata wasu makaman da ake amfani da su a yaƙin dake gudana tsakanin Rasha da Ukraine zuwa Yankin Tafkin Chadi. Buhari yace ya zama wajibi shugabannin dake yankin su tashi tsaye wajen daukar matakan da suka dace na dakile safarar kanana da manyan makaman dake kwarara zuwa yankin. Shugaban ya bayyana hakan ne a taron shugabannin ƙasashen yankin chadi a Abuja, yace babu tantama yaƙin Rasha da Ukraine tare da wasu tashe tashen hankulan da ake fama da su a yankin Sahel…
Cigaba Da KarantawaAPC Ta Tafka Babbar Asara: Surukin Buhari Ya Fice Daga Ciki
Jam’iyyar APC ta rasa daya daga cikin yan takararta na gwamna a jihar Kaduna, Sani Sha’aban Sha’aban wanda suruki ne ga shugaban kasa Buhari ya rasa tikitin takara a hannun Sanata Uba Sani. A ranar Litinin, 28 ga watan Nuwamba, Sha’aban ya sanar da ficewarsa daga APC a cikin wata wasika da ya sanyawa hannu, kuma aka rarraba ta ga manema labarai. Ya ce harkokin jam’iyyar ne suka sanya shi yin murabus, yana mai zargin cewa maimakon shayar da mutane romon damokradiyya, wasu yan tsiraru a APC reshen Kaduna sun…
Cigaba Da Karantawa