Borno: Dakarun Soji Sun Daƙile Harin Boko Haram

Dakarun Sojin najeriya sun hana mayakan Boko Haram hawa wani shinge a kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri a jihar Borno.

Sojojin sun yi arangama da maharan a musayar wuta a kusa da garuruwan Mainok da Jakana a yau lahadi .

Wani direban kasuwanci ya fada wa majiyarmu cewa lamarin ya faru ne jim kadan bayan an sassauta rufe hanyar da aka saba yi da safe.

Sojoji na yawan rufe hanya da yamma kuma suna bude ta da karfe 7 na safiyar kowace rana.

Direban ya ce wasu da ake zargin masu tayar da kayar baya ne wadanda ke shirin hawa shinge a kan hanya sannan su far wa matafiya, sojoji sun ci karfinsu.

“Muna kan hanyar mu ta zuwa Maiduguri bayan mun kwana a Damaturu sai sojoji suka tare mu a wani wuri bayan Mainok.

“Tun da farko an nemi mu koma baya kuma daga baya aka ce mu tsaya a wurin. Daga baya an yi harbi a gabanmu, wanda ya zama kamar musayar wuta. An nemi mu ci gaba bayan kimanin minti talatin da biyar, ”inji shi.
Ya ce an sanya karin sintiri a kan hanyar.

Boko Haram dai ta sanya rayuwa ta zama lahira ga wadanda ke bin wannan hanyar. A kan hanyar ne aka sace wata sabuwar amarya a makon da ya gabata amma an sake ta bayan awanni 24.

Kafin ya kawata sabbin hafsoshin rundunar a ranar Juma’a, Shugaba Muhammadu Buhari ya ba su ‘yan makonni don magance matsalar rashin tsaro da ta zama ruwan dare a kasar.

Labarai Makamanta

Leave a Reply