Bata Suna: INEC Ta Yi Barazanar Maka PDP Kotu

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Hukumar Zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi barazanar gurfanar da babbar jam’iyyar adawa ta PDP a gaban kotu, bisa zargin bata sunan shugaban hukumar Farfesa Mahmoud Yakubu. 

Sakataren yada labaran hukumar Mr Rotimi Lawrence Oyekanmi ne ya bayyana wannan barzana a birnin tarayyar kasar Abuja. 

A cewar sa jam’iyyar PDP na yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da bata sunan shugaban hukumar ta hanyar zargin sa da magudi a zaben da ya gabata da kuma saura tsarin na’urar tantance masu zabe ta BVAS da gangan kawai don samun nasarar jam’iyyar APC.

Ya ce bayan kiraye-kirayen sallamar shugaban hukumar da PDP ke yi, da kuma maka ta a kotu bisa zargin hada kai da magudi, jam’iyyar na kuma ci gaba da bata sunan shugaban hukumar a idanun duniya da angiza ‘yan Najeriya kan su tsane shi ko ma kai masa hari. 

Labarai Makamanta