Rahoton dake shigo mana daga jihar Anambra na bayyana cewar Jam’iyyar PDP tace shiri ya yi nisa na karban ɗan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, a jihar ranar Alhamis domin gangamin yakin neman zaɓe. Daraktan kamfen Atiku/Okowa na jihar Anambra, Dakta Obiora Okonkwo ne ya bayyana haka a wurin taron manema labarai ranar Laraba a Awka. Yace wannan gangamin kaddamar da yakin neman zaben PDP da zai guda a Awka a yau zai tabbatar wa duniya cewa Anambra ta PDP ce gaba ɗaya babu maganar wata Jami’yya. Okonkwo yace jirgin…
Cigaba Da KarantawaAuthor: Ibrahim Ammani
Na Yi Dukkanin Abin Da Zan Iya A Shugabancin Najeriya – Buhari
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar mai girma Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce ya yi iya bakin kokarinsa a matsayinsa na shugaban Najeriya. Shugaban ya shaida hakan ne a Amurka lokacin da yake tarban Sakatare Janar na kungiyar Abu Dhabi, Sheikh Al- Mahfoudh Bin Bayyah da mataimakinsa, Fasto Bob Roberts na Amurka, a wata ziyarar da suka kai masa. Buhari ya ce Najeriya kasa ce mai yawan al’umma da ke fuskantar kalubale daban-daban, sai dai a tsawon shekarun mulkinsa ya san cewa ya yi…
Cigaba Da Karantawa‘Yan Bindiga Sun Kaddamar Da Sabon Hari A Jihar Borno
Labarin dake shigo mana daga Maiduguri babban birnin Jihar Borno na bayyana cewar wata mata mai juna biyu, Mary Barka ta rasa ranta yayin da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, dauke da bindigu kirar AK 47 suka yi dirar mikiya kauyen Pelachiroma na karamar hukumar Hawul dake jihar Borno. Ba tare da jinkiri ba shugaban mafarautan yankin Muhammad Shawulu Yohanna yayi nasarar cafkesu gami da mika su ga shugaban ‘yan sandan yankin Hawul, Habila Lemaka. Kamar yadda Yohanna, shugaban ‘yan sa kai da mafarauta ya bayyana…
Cigaba Da KarantawaRashin Albashi: Ma’aikata Sun Tsunduma Yajin Aiki A Jihar Filato
Labarin dake shigo mana daga Jos babban birnin Jihar Filato na bayyana cewar Ma’aikatan gwamnati a jihar sun shiga yajin aikin jan kunne na kwanaki biyar wanda ya fara a ranar Litinin, 12 ga watan Disamba Ma’aikata sun yanke shawarar daina aiki na wucin-gadi bayan gwamnatin ta ki biyansu albashi tsawon watanni uku. Ma’aikatan sun kuma yanke shawarar tafiya yajin aiki saboda gazawar gwamnatin wajen sakin kudaden da ake ragewa kamar su kudaden fansho, garatuti da sauransu. A wani taron manema labarai da ya gudana a Labour House da ke…
Cigaba Da Karantawa2023: Gwamna Inuwa Ya Roki Gwambawa Da Yin Sak
Labarin dake shigo mana daga jihar Gombe na bayyana cewar Gwamnan jihar Alhaji Muhammad Inuwa Yahaya, ya roki jama’ar jihar su garzaya su karɓi Katin zabensu domin samun damar kaɗa wa APC kuri’unsu a 2023. Gwamnan yace ɗumbin ayyukan da ya zuba a mulkinsa na farko babban alama ce dake nuna dacewarsa musamman yadda ya maida hankali wajen yaye matsin da mutane ke ciki. Inuwa Yahaya ya yi wannan jawabin ne yayin kamfe a gundumomi 5 da suka haɗa ƙaramar hukumar Balanga ta arewa ranar Litinin. Da farko, gwamnan ya…
Cigaba Da KarantawaMatsalar Mai: Majalisa Ta Ba NNPC Wa’adin Mako Guda
Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Majalisar Wakilan Najeriya ta umarci kamfanin mai na kasa NNPC ya kawo karshen karancin fetur da ake fama da shi a cikin cikin mako guda. A cewar majalisa tsawon watanni ‘yan Najeriya na wahalar fetur wanda ke tasiri ga tattali arzikin kasa da jefa al’umma cikin wahala. Sannan kamfanin na bijiro da wasu dalilai a matsayin hujjar wahalhalun mai a fadin Najeriya, don haka wanna gargadi ne ga NNPC. Umarnin majalisa na zuwa ne bayan a karshen mako hukumar DSS ta bai…
Cigaba Da KarantawaZan Gina Sabuwar Najeriya Idan Na Zama Shugaban Kasa – Tinubu
Rahotannin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar ɗan takarar Kujerar zama shugaban kasa a inuwar jam’iyya mai mulki ta APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, yace da ikon Allah ‘yan Najeriya ba zasu yi da nasani ba idan suka zaɓe shi shugaban kasa a 2023. Tinubu ya ba da wannan tabbacin ne a wurin gangamin yakin neman zaɓensa da ya gudana a Kaduna ranar jiya Talata. Gangamin Kaduna somin taɓi ne na fara yakin neman zaben shugaban kasa na APC a shiyya mafi yawan kuri’u a Najeriya watau…
Cigaba Da KarantawaRanar ‘Yanci: Kungiyar “Back To School” Yakar Cin Zarafin Mata Muka Sa A Gaba – Abdul Ahmad
Sakamakon ranar da majalisar ɗinkin Duniya ta ware na ranar ‘yanci ta duniya, wata Ƙungiya mai rajin kare yaƙin mata dake Kaduna wadda a turance ake kira da suna “Back To School” ta gudanar da taro a Kaduna domin jan hankali da wayar da kan jama’a akan cin zarafin Mata. Shugaban kungiyar Abdul Ahmad ya bayyana cewar dalilin shirya wannan taron nasu shi ne domin fadakarwar da wayar da kan jama’a musamman Mata domin sanin muhimmancin kansu da kuma kare kai daga dukkanin nau’ika na cin zarafi. Ahmad ya ƙara…
Cigaba Da KarantawaBa Zan Iya Zama Dan Majalisa Ba Saboda Ban Da Hakuri – El Rufa’i
Rahoton dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewar Gwamnan jihar Nasir El-Rufai ya nuna babu shi babu zuwa majalisar tarayya ta kasa bayan kammala wa’adin Mulki. An san Gwamnoni da yin takarar Sanata idan sun gama wa’adinsu a jihohi, sai dai anashi ɓangaren Malam Nasir El-Rufai yana cewa ya sha bam-bam da sauran gwamnoni yace bai da hakuri da jajircewar da ake bukata wajen aikin majalisa. Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a wajen wani taron ‘yan majalisa da cibiyar nazarin aikin majalisa da damukaradiyya watau NILDS ta…
Cigaba Da KarantawaTakaita Cire Kudi Zai Rage Wa ‘Yan Siyasa Sharholiya – Sanusi
Khalifa Muhammad Sanusi , ya ce matakin da babban bankin Najeriya ya dauka na takaita cirar kudaden zai fi yin tasiri a kan `yan siyasa kasar fiye da talakawa. Ya bayyana hakan ne a karshen karatun Madaris da ya saba yi duk karshen mako. Ya ce `yan siyasar kasar na amfani da kudi a lokacin zabe don sayen kuri’un jama’a, lamarin da ke haifar da koma-baya ga kasar. Muhammadu Sanusi na II ya ce “abin takaici ne yadda mutane za su yi shekara hudu suna kwasar dukiyar al’umma, suna barin…
Cigaba Da KarantawaSai An Biya Miliyan 100 Kafin Mu Saki ‘Yan Matan Kwalejin Yawuri – ‘Yan Bindiga
Fitaccen ɗan ta’addan jihar Zamfara Dogo Gide da yayi garkuwa da dalibai mata ‘yan kwalejin Yawuri dake jihar Kebbi ya rantse ba zai saki sauran wadanda suka rage a hannunsa tare da malaman su har sai an kai masa diyyar naira miliyan 100 da ya bukata. Wannan matsayi ya biyo bayan wani sautin hirar da aka nada tsakanin wani daga cikin mahaifin dalibar dake hannunsa da mahaifiyarsa wadda ta bukaci ya sake sauran wadanda yayi garkuwar da su. Gide wanda yayi kaurin suna wajen kai munanan hare hare yana hallaka…
Cigaba Da KarantawaTinubu Ya Ziyarci Birnin Gwari Kafin Fara Kamfe A Kaduna
Labarin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar ɗan takarar shugabancin ƙasa a karkashin jam’iyya mai mulki ta APC Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci Birnin-Gwari kafin fara yakin neman zabensa a Kaduna. Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da tawagarsa sun isa jihar Kaduna inda za su gudanar da yakin neman zabensa a jihar ta Kaduna a ranar Talata. Tinubun ya samu rakiyar abokin takararsa Sanata Kashim Shettima da babban daraktan yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Filato, Simon…
Cigaba Da KarantawaBoko Haram: Karya Ce Babu Inda ‘Yan Ta’adda Za Su Boye A Sambisa – Atiku
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar ɗan takarar shugabancin ƙasa a babbar jam’iyya adawa ta PDP Atiku Abubakar, yace duk ƙarya ce ake yi kawai, amma babu wani surƙuƙin dajin da ‘yan ta’adda za su iya ɓoyewa a Dajin Sambisa, a ce wai an kasa gano inda su ke. Atiku ya ce ya shiga dajin, amma babu komai daga ciyayi, sai kalage da gezoji kawai. Ya ce kan sa na ɗaurewa ganin yadda ake ta gaganiya da Boko Haram, amma an kasa ganin bayan su…
Cigaba Da KarantawaKano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Wa Abduljabbar Hukunci
Rahotannin dake shigo mana daga jihar Kano na bayyana cewar Kotun Shari’ar Musulunci da ke birnin ta saka ranar 15 ga watan Disamban 2022 don yanke hukunci kan tuhume-tuhumen da ake yi wa malamin nan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara. Gwamnatin Kano na tuhumar shehin malamin da yin ɓatanci ga Annabin Musulunci Muhammadu S.A.W. kuma an tsare shi tun daga watan Yulin 2021. Abduljabbar zai sake bayyana a gaban Mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola na kotun da ke Ƙofar Kudu ne bayan ƙungiyar lauyoyi masu bai wa marasa gata kariya ta…
Cigaba Da KarantawaNa Bar PDP Har Abada – Obasanjo
Tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo, a ranar Asabar, ya bayyana cewa ba zai taba komawa jam’iyyar adawa ta PDP da siyasa ba gaba daya a rayuwarsa. Ya bayyana hakan ne yayin hira da shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu da sauran masu fada a ji a jam’iyyar da suka ziyarcesa ranar Asabar bayan ganawar sirrin da suka yi, a gidansa dake birnin Abeakuta na jihar Ogun. “Na fita harkar siyasa kuma babu abinda zai iya mayar da ni. Duk wanda ke son shawarata, zan bada saboda amfanin Najeriya.” “Duk abinda nayi…
Cigaba Da KarantawaZan Yi Mulki Na Adalci Idan Na Lashe Zabe – Tinubu
Labarin dake shigo mana daga birnin Ibadan na Jihar Oyo na bayyana cewar a ranar Lahadi, 11 ga watan Disamba, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu, ya ba yan Najeriya tabbacin cewa zai zamo mai gaskiya da adalci ga kowa. Tinubu ya bayar da tabbacin ne yayin da yake jawabi a wani taro da shugabannin Musulunci daga kudu maso yamma a Ibadan, babban birnin jihar Oyo a ƙarshen mako. Dan takarar na APC ya yaba ma shugabannin addini a kasar kan addu’o’i da suke ci gaba…
Cigaba Da KarantawaShekau Ya Mutu Ya Bar Mata 83 A Duniya – Kwamandojin Boko Haram
Rahotannin dake shigo mana daga Maiduguri babban birnin Jihar Borno na bayyana cewar wasu tsoffin Kwamandojin Boko Haram sun sanar da cewar shugabansu Abubakar Shekau ya mutu ya bar kwarkwara 83, lokacin da ya bar duniya. Mai ba Gwamnan Jihar Borno shawara a kan harkokin tsaro, Janar Abdullahi Ishaq ya sanar da wannan labari, yayin da ya bayyana cewar wasu tubabbun Kwamandojin Boko Haram da suka aje makamansu ne suka shaida masa. Janar Ishaq ya ce lokacin da suka karbi wasu daga cikin tubabbun a garin Bama ne daya daga…
Cigaba Da KarantawaBuhari Bai Da Masaniya Kan Kwamitin Da Gudaji Ke Ikirarin Shugabanta – Garba Shehu
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan wani ikirari da kwamiti na musamman da shugaban kasar ya kafa domin ya gudunar da bincike a kan cajin cirewa da ajiyar kudi a asusun banki ƙarƙashin jagorancin Honorabul Gudaji Kazaure. Shugaban kwamitin, Gudaji Kazaure ya yi zargin cewa wasu hukumomin da binciken ya shafa suna kokarin hana ruwa gudu game da aikin nasa, da kuma hana shi ya mika wa shugaba Muhammadu Buhari rahotonsa. A cewar kwamitin wanda aka dora…
Cigaba Da KarantawaMatsalar Tsaro: INEC Za Ta Sauya Wa Rumfunan Zabe 357 Waje A Katsina
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta ce za ta mayar da rumfunan zabe 357, PUs, zuwa wuraren da babu tsaro saboda kalubalen tsaro a jihar Katsina. A cewar hukumar, ta dauki matakin ne domin bai waduk ‘yan gudun hijira, da ke jihar damar kaɗa kuri’unsu a zaben 2023. Kwamishinan zaɓe na jihar, Farfesa Ibrahim Yahaya Makarfi ne ya bayyana haka a yayin wani taron masu ruwa da tsaki a yau Juma’a a Katsina. Ya bayyana cewa, dokar zabe ta 2022 ta yi tanadin tsare-tsare a bayyane da…
Cigaba Da KarantawaBauchi: An Damke Malamin Da Ya Soki Izala Kan Harka Da ‘Yan Siyasa
Labarin dake shigo mana daga jihar Bauchi na bayyana cewar Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar sun kama gami da tsare wani malamin addinin musulunci mazaunin garin Bauchi mai suna Abubakar Baba Karami bisa zarginsa da wasu kalamai kan ‘kungiyar izala inda ya nuna malamanta suna mu’amala da ‘yan siyasa. Malamin wanda aka fi sani da Afakhallah yayi wannan maganar ne akan mumbarin masallacin Juma’a a wani masallaci a jihar Bauchi a ranar 18 ga watan Nuwanban 2022. Ya bayyanna sunan Kabir Muhammad Gombe da Abdullahi Bala Lau da Ahmed Sulaiman…
Cigaba Da Karantawa