Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Hukumomi sun bayyana cewar ƙasar ta daƙile yunƙurin kutse ko hare-hare a kan hanyoyin sadarwa na intanet har kimanin miliyan 13 a lokacin zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar. Babban daraktan hukumar bunƙasa fasahar sadarwa ta Najeriya, wato NITDA, Kashifu Inuwa AbdulLahi, shi ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa da BBC, inda ya ce an samu nasarar ce sakamakon wasu cibiyoyi da aka kafa don yaƙi da kutsen ta intanet da kuma wani kwamiti na musamman da…
Cigaba Da Karantawa