2023: Gowon Ya Yi Ishara Ga Shugaban Da Ya Kamaci Najeriya

Tsohon Shugaban Ƙasa na mulkin soja, Janar Yakubu Gowon, ya bayyana cewa sai mutumin ƙwarai, sahihi ya kamata ya shugabanci Najeriya a 2023, ba rubabi-rubabi ba.

Gowon ya furta haka ne a ranar Juma’a, lokacin da ƙungiyar Tallata Takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo ta kai masa ziyara a gidan sa da ke Asokoro, Abuja.

Ƙungiyar mai suna Progressive Consolidated Group, sun Kai masa ziyarar ce domin su sanar da shi aniyar su ta ganin cewa zaɓen Osinbajo shi ne mafita kuwa hanyar fidda Najeriya daga ƙuncin da ‘yan ƙasar ke ciki.

Gowon ya ce duk da ba ya yin katsalandan cikin harkokin siyasa, amma bai ba zai ƙi yi wa ‘yan Najeriya nasiha ba cewa wajibin dukkan kowa da kowa ne su ga cewa sun haɗa kai an samu ci gaba, zaman lafiya da shugabanni nagari daga sama har ƙasa.

Yayin da Gowon ke bayani, ya ce ya kamata a sani cewa duk sharri da tuggu da ƙulle-ƙullen da za a yi don a hana wani nasara, to Ubangiji ne ke ƙaddara wanda zai yi mulki.

Ya kuma ja hankulan masu kafafen yaɗa labarai su fi maida hankali wajen tabbatar da haɗin kan ƙasar nan.

Sannan kuma ya ce ba za a kai gaci ba har dai masu neman muƙamai wato ‘yan siyasa sun cusa kishi su da magoya bayan su, maimakon a riƙa ɗin bada ƙarfi wajen neman muƙamai wurjanjan.

Tawagar da ta kai wa Gowon ziyasa na ƙarƙashin Baraden Lafiya, Musa Kwande da Babban Kodinetan PCG, Ahmed Kari.

Bayan yin jawabai sun kuma gana asirce da Gowon.

Labarai Makamanta

Leave a Reply